Gwamnatin Jihar Kogi ta baiwa Hukumar Yaki da yi wa Tattalin Arzikin Kasa Ta’annati (EFCC) wa’adin sa’o’i 48 da ta nemi afuwa tare da janye wata magana da ta yi akan gwamnatin jihar cewa ta ajiye Naira biliyan 20 a wai asusun albashin ma’aikata da ke wani bankin kasuwanci da nufin samun riba.
A wani jawabi da ya yiwa manema labarai, Kwamishinan Yada Labarai, Kingsley Fanwo, ya ce gwamnatin jihar ba ta bude ko kirkiri wani asusun ba.
“Ina so in tabbatar muku da cewa bayan sa’o’i 48 daga yau Lahadi, idan suka ki janye kalaman da suka yi na rashin gaskiya, karya, siyasa, rashin da’a, za mu kai su kotu,” in ji Kwamishinan.
Haka zalika kwamishinan ya kalubalanci hukumar yaki da cin hanci da rashawa da ta samar da hukunce-hukuncen asusu da bayanan wadanda suka gudanar da asusun.
Hakan dai na zuwa ne kamar yadda gwamnatin jihar Kogi ta ce ta samu martanin bankin wanda ya wanke su daga gudanar da asusun.
A cewar jihar, gwamnati na da isassun shaidun da ake zargin hukumar EFCC da za ta kai kara kotu.
“Gwamnatin jihar Kogi a halin yanzu ba ta aiki ko kula da asusun ajiyar kuɗi da bankin Sterling.
“Babu wata takarda da gwamnatin jihar Kogi ta bayar na bude asusu mai lamba 0073572696 da bankin Sterling. Fanwo ya kara da cewa, asusun bankin Sterling 0073572696 asusun madubi ne na cikin gida da bankin ke sarrafa shi domin gudanar da ayyukan ceto albashin jihar Kogi.
Jaridar Dimukuradiyya ta rawaito Hukumar EFCC a cikin wata takardar shaida mai sakin layi 13 na goyon bayan wata bukata ta bayyana cewa ta samu sahihan bayanai kuma kai tsaye wanda ya kai ga gano asusun bisa la’akari da kudaden haramun na asusun da ke cikin bankin Sterling.