Nigeria na bukatar kashi 95 na ‘network’ a ko’ina kafin ta yi amfani da tura sakamakon zabe ta yanar gizo, inji Orji Kalu

Kalu yace 'Network din da Nigeria ke dashi a halin yanzu yayi karanci kuma bashi da karfi.

Shugaban masu Horaswa na Majalisar Dattijai ta Nigeria, Sanata Orji Kalu yace Nigeria na bukatar ya kasance a kalla akwai kashi 95 na layukan sadarwa wato-Network a fadin kasar, domin tura sakamakon zabe ta hanyar yanar gizo a kasar.

Orji Kalu ya bayyana haka a lokacin da yake wata zantawa da Kamfanin Dillancin Labaru na Kasa wato-NAN.

Idan dai ba’a manta ba majiyar jaridar Dimokuradiyya a ranar 15 ga watan Juli ta ruwaito cewa, Sanatoci 52 ne suka kada kuri’ar gudanar da zabe ta hanyar yanar gizo a Babban zabe mai zuwa na Shekarar 2023, a yayinda Sanatoci 28 suka kada kuri’ar rashin amincewa akan gudanar da hakan, inda Sanatoci 28 basu samu zaman Majalisar daya gudana.

“Kamar Abia ta Arewa inda na futo, babu layukan sadarwa a wasu wuraren, akwai dai kashi 43, to taya zamu gudanar da zabe akan hakan, nayi imani akan tura sakamako ta hanyar yanar gizo, amma ina so inyi kira ga Hukumar NCC da tayi gaggawar kawo fasahoh,i domin tabbatar dacewa akwai layukan sadarwa a ko’ina, nayi imani akan wannan hanyar domin akwai gaskiya acikin ta.

“duk abunda zanyi sai na tabbatar zai amfani dukknanin yan Nigeria,” inji Kalu.

 

Next Post

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Archives

Welcome Back!

Login to your account below

Retrieve your password

Please enter your username or email address to reset your password.