Kungiyar likitocin Najeriya ta yabawa mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo bisa amincewa da tsarin kiwon lafiyar Najeriya da ya sanya aka yi masa tiyata a kasar.
Jaridar Dimokuraɗiyya ta ruwaito cewa mataimakin shugaban kasar ya samu nasarar yi masa tiyata, a wani asibitin Duchess na kasa da kasa dake Ikeja a Legas.
A cewar wata sanarwa da hukumar gudanarwar asibitin ta fitar dauke da sa hannun daraktan kula da lafiya, Dokta Adedoyin Dosunmu-Ogunbi, ta ce tawagar da ta kunshi kwararrun Likitoci shida ne suka gudanar da aikin.
Sanarwar ta ci gaba da cewa, “A yau ne Mataimakin Shugaban Tarayyar Najeriya, Farfesa Yemi Osinbajo, SAN, GCON, ya kwanta a Asibitin Duchess International Hospital GRA, Ikeja, Legas, sakamakon rauni da yake fama da shi a kafarsa.
A halin da ake ciki, NMA a wata sanarwa da ta fitar mai taken ‘fatan samun sauki gare shi’ ta ce likitocin Najeriya na yi wa mataimakin shugaban kasar fatan samun sauki cikin gaggawa.
Sanarwar ta ce, “Hukumar NMA na fatan alkhairi da godiya ga Allah da ya ƙaddara yin aikin ga mataimakin shugaban kasa Farfesa Yemi Osinbajo ta hanyar yi masa tiyata.
Dukkan Likitocin Najeriya na yi masa addu’ar samun sauki cikin gaggawa da kuma samun cikakkiyar lafiya.
“Muna kira ga sauran masu rike da mukaman siyasa a Najeriya da su yi koyi da Mataimakin Shugaban kasa su kawo karshen yawon bude ido na likitanci. Lokaci ya yi da za mu gyara tsarin kiwon lafiyar mu mai rauni don amfanin talaka da tattalin arzikinmu. Yanzu lokacin daukar mataki ne.”