Majalisar matasa ta ƙasa NYCN ta yabawa asusun tallafawa manyan makarantun gaba da Sikandire a Nigeria, bisa kiran da yayi ga gwamnatin tarayya wajen kara yawan kuɗin da take baiwa asusun.
NYCN ta ce wannan kiran Namijin kokari ne da asusun yayi, wanda kuma zai yi amfani da kudin ne ta hanyar da ta dace wajen samar da kyawawan yanayi na karatu ga dalibai a Nigeria.
Sakataren tsare tsare na kungiyar na kasa Comrade Z. Olawale ne yayi wannan yabon cikin wata sanarwa da ya fitar mai dauke da sa hannunsa. Inda yace hakan abun cigaba ne da shugaban asusun Farfesa Bogoro ya kawo.
Daga nan sai Kungiyar matasan ta bukaci gwamnatin tarayya da ta kara yawan kuɗin da take baiwa asusun na Tetfund, domin kuwa kwalliya na biyan kudin sabulu.