Daga Abdullahi Kebbi
Hukumar zaben kasar Malawi ta fitarda sanarwar cewa Peter Mtharika ne ya lashe zaben shugaban kasa da aka gudanar a kasar.
Shugaba Mutharika yayi nasarar kakkebe abokin adawarsa Lazarus Chakwera na jam’iyyar MPC da kaso 38.57 na kuri’unda yan kasar suka jefa.
Inda abokin adawarsa Chakwere ya samu kaso 35.4 na kuri’unda yan kasar suka jefa.
Jam’iyyar MPC dai ta kasance babbar Jam’iyyar Adawa a kasar malawi.
Kamar yadda shugabar hukumar zaben kasar ta bayyana wato mai shari’a shari’a Jane Ansah ta bayyana cewa mutum miliyan 5.1 ne suka jefa kuri’un.
Hukumar zaben dai tace ta saurari dukkan korafe korafe daga kowacce jam’iyya, sai dai tana mai cewa ta tabbatarda anyi zabe mai sahihanci tare da bayyana muradun kasar Malawi.