Wakilinmu Shu’aibu Ibrahim Gusau
Shugaban rundunar Operation Hadarin Daji, manjo ganar Jide Ogun Lade, yayi Kira da kakkausar murya ga ‘yanbindigar jihar zamfara, dasu Mika makamansu cikin awa ashirin da hudu.
Shugaban ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labaru a ofishin sa da ke gusau babban birnin jihar zamfara.
Ya Kara da cewa Yana Kira ga duk wani Wanda yake da Yaro ko dan’wa ko makwabci, ko Kuma wani Wanda yasan makwabcinsa ne Kuma Yana tare da wadannan barayi, to a kirasu a sanar dasu cewa an Basu awa ishirin da hudu su Mika makamansu.
Jide, ya Kara da cewa wannan karo zasu fitowa Barayin ta inda Basu zata ba, yace zasu bisu har mabuyarsu, domin a cewarsa a baya sun fahimci barayin suna shigowa kauyuka suna sajewa da mazauna kauyukan.
Sai dai bayan kammala bayanan nasa ya nunawa manema labaru wadansu bindigogi da yaranshi suka Sami nasaran karbarsu daga hannun ‘yanbindiga.
Wadanda suka hada da Bindiga AK 47 guda11 da Kuma Bindiga ta gargajoya gudanar 14 da harsashi 2437 da karamar Bindiga gudanar biyu ta hannu da dai sauran kayayyaki.
Shugaban rundunar ya bukaci al’ummar jihar zamfara musamman mazauna kauyukan dasu Basu goyon baya da hadin Kai don samun nasara kan wannan yaki da zasuyi.
Sai dai shugaban yayi Kira ga ‘yanjarida dasu rika Yi masu adalci suna tuntubarsu domin tantance duk wani bayani da suke nema , amma yace kada ace an nemesu ba’a samesu ba domin sun bada lambobin ways da jama’a zasu rika kiransu, saboda ko ta kwana.