Daga Zahra Sarki
Tuni shirye shirye yayi nisa na ganin an sasanta rikicin dake tsakanin jagorori guda biyu dake ikirarin shugabantar majalisar dokokin Jihar Bauchi.
Matukar wadannan bangarori guda biyu suka sasanta, hakan zai bada dama wurin gudanar da ayyuka a majalisar dokoki a Jihar.
Kuma hakan zai baiwa Gwamnati a matakin majalisar zartarwa damar aiwatar da ayyukanta kamar yadda ya kamata.
Shugaban majalisar dokoki na daya bangaren Abubakar Sulaiman, shi ne ya bayyana hakan yayin zantawarsa da yan jaridu a nan jihar Bauchi, inda ya bayyana cewa tuni shirye shirye yayi nisa don ganin ya sulhunta da daya bangaren, inji shi.
ya cigaba da cewa wasu daga cikin ‘yan Majalisun da ke daya bangaren ‘yan adawa da shi tuni suka bada Kai, Abubakar Sulaiman, yayi kira ga daya bangaren da suke ikirarin jagoranci da su zo a kauda bambancin da suke da shi a tsakani a hada kai a yi aiki wa al’ummar jihar Bauchi.
“Ni dan siyasa ne kuma abinda ya faru a cikin siyasa ne za muyi amfani da hanyar Siyasa muga cewa mun gyara abin in Allah ya yarda, inji shi.
Duk wadanda basuji dadin abinda ya faru ba za muyi kokari mu samesu duk abubuwan da ya kamata muyi na lallami da kuma kokarin a fahimtar dasu gaskiyan al’amari su fahimta, Wannan mun riga mun fara”.
Abubakar Sulaiman ya baiyana cewa wata babbar kotu a nan jihar Bauchi, ta bada wani umurni na doka da ya haramta wa kawuwa shehu damina, da tukur Ibrahim, cigaba da Ayyana kansu a matsayin kakakin majalisa da mataimakinsa har zuwa lokacin da za’a kammala sauraron karan dake gaban kotun.
Abubakar, ya Ce Shi Shugaban masu rinjaye da sauran mukamai an barshi ne ga mambobin da suka fi rinjaye a majalisan, dan haka samun yin sulhun a daidaita shine zai ba mu damar gyara wannan matsalar dake tsakani da ma duk wani abu da ya shafi haka.
Da yake tankawa kan wannan lamari kakakin majalisa dake daya bangaren Alhaji Kawuwa shehu Damina, ya ce har ya zuwa yanzu babu wata takarda daga kotu da take bayyana dakatar da shi a matsayin kakakin majalisa ta tara.
Idan jam’iyyar mu ta APC wanda ita muka biyo muka hau muka zama abin da muka zama,Ta zo ta kira ta ce kowa ya hakura ko kuma ta ce a zo a zauna a yi gyara bisa abin da ya faru, koma dai me ta Ce a yi za muyi mata biyayya, inji shi.
Kawuwa shehu Damina, ya ce ya zuwa yanzu babu wani tuntuba da akayi musu na ganin cewa an sasanta tsakaninsu, ya cigaba da bayyana cewa ‘ya’yan jam’iyyar APC Guda goma sha takwas da suke bangarensa suna nan akan bakansu na biyayya ga duk abinda jam’iyyar APC ta ce a kan wannan matsaya da ake a nan jihar Bauchi.