By Abbas Yakubu Yaura
Rundunar ‘yan sandan Najeriya a ranar Litinin ta bude shafin ta na yanar gizo don daukar ma’aikatan ‘yan sanda na shekarar 2021.
An bayyana hakan ne a wata sanarwa mai dauke da sa hannun jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sanda, Frank Mba a hedikwatar hukumar dake Abuja.
A cikin sanarwar mai taken, ‘daukar ma’aikata na shekarar 2021, zuwa rundunar ‘yan sandan Najeriya, rundunar ta bayyana cewa wadanda suka yi nasara za a shigar dasu a matsayin ‘yan sanda.
Za a buɗe tashar aikace-aikacen daukar ma’aikatan na tsawon makonni shida daga Litinin,29 ga watan Nuwamba na shekarar 2021 zuwa ranar Litinin 10 ga watan Janairu.
Bayan kammala aikace-aikacen, za a gayyaci wadanda sukayi nasara don yin gwajin jiki daga ranar 10 ga watan Janairu zuwa ranar 24,