By Abbas Yakubu Yaura
Gwamnan jihar Ogun, Dapo Abiodun, a ranar Litinin din da ta gabata yace gwamnatinsa za ta shirya wata doka da zata ba da shawarar dauri ga shugabannin hukumomin dake kula da gine-gine idan wani gini ya ruguje a jihar a karkashin kulawarsu.
Gwamnan ya bayyana hakan ne a yayin taron kwamitin baitul mali kan tsarin kashe kudade na matsakaicin wa’adi na shekarar 2022-2024 da kuma kasafin kudin shekarar 2022 a Abeokuta, babban birnin jihar.
Sannan yace, “Na fito da wata doka da zata tura ma’aikata masu harkar gine-gine gidan yari. Ma’aikata a hukumomin dake da alhakin kula da gine-gine suna da wuyar karbar cin hanci”. in jishi
“Zan tabbatar da cewa akwai wani abu a dokar mu da zai tura shugabannin hukumar kula da gine-gine gidan yari idan wani gini ya ruguje a jihar Ogun a karkashin kulawarsu.
“Damuwa da wadanda ke da alhakin kula da ginin bai kamata kawai ya zama kudaden shiga ba amma don tabbatar da tsari da ayyuka mafi kyau bisa ga ka’idojin gine-ginen Jiha.”
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa Abiodun ya bayyana cewa gwamnatinsa ta kara yawan kudaden shiga da ake samu a cikin gida tare da samun kudi fiye da kowace gwamnati a cikin shekara guda.
Ya bayyana cewa gwamnatinsa ta yanke shawarar tallafawa kiran da wasu gwamnatocin jihohi suka yi na a karbo Haraji mai daraja don tabbatar da cewa wadanda suke samar da VAT, sun karba kuma su ji dadinsa.“Kamfen ɗin VAT yana cikin ruhin sake fasalin da tsarin tarayya na kasafin kuɗi,” in ji shi.