Sallah: An saki fursunoni 222 a Katsina
Gwamnatin jihar Katsina ta saki fursunoni 222 da ba za su iya biyan tarar da kotuna daban-daban suka yanke musu ba gabanin bikin Sallah.
Gwamnan jihar, Malam Dikko Umaru Radda, ya ce manufar ita ce rage nauyin fursunoni a fadin gidajen gyaran hali na jihar a cikin watan Ramadan da kuma bukukuwan Sallah mai zuwa.
KARANTA WANNAN LABARIN:Ban taba tunanin cewa zan samu mataimakan gwamnoni guda biyu ba – Obaseki
Babban Lauyan jihar kuma kwamishiniyar shari’a Fadila Muhammad Dikko, ta bayyana hakan a wata sanarwa.
Ta ce mutane 222 da suka ci gajiyar tallafin, an zabo su ne bayan an tantance su sosai, biyo bayan shawarwarin da gwamnatin jihar ta ba su na ta shiga tsakani.
“Ana sa ran aikin alherin da Gwamna ya yi zai rage cunkoso a wadannan wuraren tare da baiwa fursunonin da aka sako damar cin moriyar bikin Sallah tare da ‘yan uwansu,” in ji Fadila.
Da take yabawa Gwamna Radda kan wannan shiri, babbar mai shigar da kara ta Katsina ta bayyana cewa an zabo wadanda suka ci gajiyar shirin ne daga cikin fursunonin da ake tsare da su bisa kananan laifukan kasuwanci da kuma wadanda ba na babban gida ba.
A wani labarin kuma:Eid-el-Fitr: FG ta amince da Alhamis a matsayin ƙarin hutun Sallah Ƙarama
Gwamnatin tarayya ta amince da ranar Alhamis a matsayin karin hutu domin murnar sallar Eid-El-Fitr ta bana.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da Dr Aishetu Gogo Ndayako, babban sakatare na ma’aikatar harkokin cikin gida ya fitar ranar Talata.