Kwamishinan zabe na hukumar zabe mai zaman kanta a jihar Neja, Farfesa Sam Egwu, ya bayyana cewa wa’adin sama da kwamishnonin hukumar 20 ne zasu kammala wa’adin aikin su a watan Yuni da Agustan dake tafe, wato dai ‘yan watanni kafin zaben 2023.
Farfesa Sam Ya bayyana hakan ne a ranar Litinin da ta gabata yayin da yake zantawa da manema labarai bayan taron masu ruwa da tsaki na farko a hedkwatar hukumar da ke Minna.
Ya ce, “Ya zuwa karshen watan Yuni, kimanin kwamishinonin zabe 20 ne za su tafi wanda kuma za su hada da wadanda suka yi wa’adi na biyu, don haka ba za su cancanci a sake nada su ba. Kuma a watan Agusta, wani sashe kuma zai tafi. ”
Farfesa Egwu, wanda yana cikin wadanda wa’adinsu zai kare, bayan da ya yi wa’adi na biyu a matsayin kwamishinan, ya jaddada bukatar a nada sabbin mutane a kan lokaci domin tabbatar da cewa ba a kawo cikas ga harkokin zabe.
Ya ce samar da mafita shi ne babban jigon magance matsalolin siyasa da na zabe a kasar, inda ya koka da yadda rashin tsari, dimokuradiyyar cikin gida da cin amana a tsakanin jam’iyyun siyasa ya zama wani rukunin tsarin dimokuradiyya da zabuka a Najeriya.
Egwu ya yi kira da a tallafa wa sarakunan gargajiya, kungiyoyin farar hula da kuma kafafen yada labarai wajen wayar da kan masu kada kuri’a su yi amfani da ‘yancinsu na ‘yan kasa a zabe mai zuwa.