Sarkin Rano Ya Dakatar Da Hakimai Biyu,
A ranar Alhamis ne Mai Martaba Sarkin Rano, Alhaji Tafida Ila Autan Bawo, ya dakatar da wasu Hakiman Masarautar guda biyu a kan nuna halin rashin da’ar da suka yi wa Masarautar.
Hakiman biyu da aka dakatar su ne, Hakimin Bebeji, Alhaji Haruna Sanusi da Hakimin Tudun wada, Dakta Bashir Muhammad.
Masarautar dai ta Rano tana daya daga cikin sabbin Masarautu hudu da gwamnatin Jihar ta Kano ta kirkiro a ranar 8 ga watan Mayu, wadanda kuma suke fuskatar shari’a a kotu a halin yanzun kan halascin kirkiran na su.
Sauran Masarautun uku su ne, Masarautar Karaye, Bichi da kuma Masarautar Gaya.
An bayyana dakatar da Hakiman ne a cikin wata sanarwa da Sakataren Masarautar, Muhammad Idris Rano ya fitar, ya kuma aike ta ga Hakiman biyu.
Sanarwar ta ce, an dakatar da su ne a bisa nuna rashin biyayya da Hakiman biyu suka yi wa Masarautar da aka kafa ta a bisa shari’a, a sa’ilin da suka ki su halarci bukin Sallah da aka kammala a Masarautar kwanan nan, duk kuwa da gayyatar su da aka yi zuwa wajen bukin.
Sarkin na Rano, ya kuma ya tube rawunnan da ke kawunansu na, Dan Galadiman Kano, daga kan, Haruna Sanusi da Dan Kadai Tudun Wada, daga kan Dakta Bashir Muhammad.
A cewar Sakataren Masarautar, tuni ma an sanar da ma’aikatar kula da Wannan sha’ani