Hana mahukuntan Saudi Arebiya barci shekara guda bayan kisan gillar da jami’an leken asirin kasar suka yi wa fitaccen dan jarida Jamal Khashggi a ofishin jakadancin kasarsa da ke kasar Turkiyya.
DW sun labarto cewa; kokarin da Yarima mai jiran gadon mulkin Saudiya Muhammad Bin Salman yake ta yi na wanke kansa daga kisan gillar da jami’an tsaronsa suka yi wa Khashoggin dai ya ci tura, yadda ganawar da ya yi ta yi da kafofin watsa labarai, da kashe miliyoyin daloli wajen gyara sunansa a duniya da ma jawaban da ya yi ta yi na nesanta kansa daga kisa, duk sun gaza wajen dawo da kimarsa da mutuncinsan da ya zube, wanda ada ake mai kallon matashin da ya tashi haikan wajen kawo sauyi na gari a kasar ta Saudiya da ta yi kaurin suna wajen bin ra’ayin mazan jiya.
Koda a makon da ya gabata, a wata ganawar da ya yi da gidan TV CBS na Amurka a ya aminta da daukar alhakin yin kisan a matsayinsa na jagora, sai dai ya musanta ba da umarninin a yi kisan:
“Yar jaridar ce take tambayarsa ko shi ya ba da umarnin a kashe Kashoggi, sai ya kada baki ya bada amsar cewa, ko kadan ban yi hakan ba. Wannan mummunar jaruma ce da aka tafka. Amma dole in dauki alhakin tafkata da aka yi, tunda wadanda suka aikata laifin ma’aikata ne na kasar Saudiya. Me ka ke nufi da ka dauki alhakin laifin? Sai ya ce, ina nufin a matsayina na jagora’ don laifin da ‘yan kasata suka tafka nike da alhakin hana sake aukuwar irin wannan aikin ta’asa nan gaba.”
Wani bincike mai zaman kansa da Jami’ar MDD, Aneeyes Kalamar ta gudanar kan kisan Khashoggin dai ya zargi Yariman da masaniya, mai yiwuwa ma shi ya ba da umarnin yin kisan, a ya yin da suma ‘yan majalisar Amurka da jami’an leken asirin Amurka da na Birtaniya, bincikensu ya kai ga cimma irin wannan sakamakon.
Yadda shugaba Erdogan na Turkiyya ya tsaya kai da fata wajen ganin an bi kadi da ma hukunta hakikanin wadanda ke da alhakin kisan Kashoggin dai, na kara tayar wa kasar ta Saudiya da liki:
“Idan Yarima Muhammad Bin Salman ba shi da masaniya kan kitsa wannan kisan to me zai sa shi kama mutane 20 da yi musu shari’a a boye, ba zai bayar da amsa ga wannan tambayar ba, dama tambayar da muke ta yi kan ko ina suka cusa gawar Jamal Kashoggi.”
Yunkurin da Bin Salman ya yi tayi na karkata ga zuwa kasashen nahiyar Asia da gabashin duniya don samun sabbin kawayen , shi ma bai haifar da da mai ido ba, wajen mai da shi cikin dangi, bayan mai da shi saniyar ware da dari-darin da shugabanin kasashen duniya ke yi da shi.