Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya gana da abokan karatunsa na firamare da sakandare a garin Daura na jihar Katsina a yau Talata.
A cewar wata sanarwa da babban mai taimaka masa na musamman kan harkokin yada labarai Malam Garba Shehu ya fitar, shugaban ya nemi jin dadin kowa da kowa da lafiyarsa da danginsa.
Ya ce sun yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu a tsakanin shekarar da ta gabata, lokacin da suka hadu da kuma na bana.
Kakakin shugaban kasar ya ce shugaba Buhari ya bayyana farin cikinsa da jin dadin ganawar, inda ya ce ya samu irin yadda ya saba tun suna kanana.
Ya kara da cewa, sun dan jima suna hira, suna ta tattaunawa a kan lokutan makaranta, sun yi ta tunowa da yawa.
Shehu ya ce shugaban ya godewa ‘yan makarantar bisa girmamawa da kuma jin dadin da suke masa wanda suka rike a ko da yaushe.
Ya ce shugaban kungiyar masu fada aji, Sanata Abba Ali ya yaba da irin sadaukarwar da shugaban kasa yake yi, ya kuma bukace shi da ya ci gaba da mai da hankali kan al’ummar kasa wanda a cewarsa ya fi kowa muhimmanci.
Shehu ya kara da cewa sun mika wa shugaban kasa kyauta kuma sun hada shi da wani hoton kungiya mai mantawa.