Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya yi kakkausar suka kan kisan gillar da aka yi wa Cif Oyibo Chukwu, dan takarar sanata na jam’iyyar Labour a mazabar Enugu ta Gabas da kuma mai taimaka masa, Tribune Online ta rawaito.
Wata sanarwa da mai baiwa shugaban kasa shawara na musamman kan kafafen yada labarai Femi Adesina ya fitar a ranar Juma’a, ta ce shugaban ya bayyana imanin cewa wadanda suka aikata wannan aika-aika, a Awkunanaw dake karamar hukumar Enugu ta Kudu a jihar Enugu, ba su da mutunci. rayuwar dan Adam da mutunci, don haka sun cancanci fushin adalci na halitta da na Ubangiji.
KARANTA WANNAN LABARIN: Zabukan Najeriya: Majalisar Dinkin Duniya Ta Bukaci A Mutunta Yarjejeniyar Zaman Lafiya
Ta ce shugaba Buhari ya tabbatar da kudurin sa na yin zaben da ba a tashe tashen hankula.
Ya tunatar da duk ‘yan siyasa cewa zabin masu zabe ne ke da muhimmanci, don haka duk ‘yan Najeriya da suka cancanta su jajirce wajen gudanar da ‘yancinsu na ‘yan kasa ba tare da wata fargaba ba.
Shugaban ya umurci jami’an tsaro da su bi diddigin wadanda suka aikata wannan danyen aikin, kamar yadda ya jajantawa iyalan wadanda aka kashe, kungiyar lauyoyin Najeriya (NBA) da kuma Labour Party (LP).
Shugaba Buhari ya yi addu’ar Allah ya jikan wadanda suka rasu, ya kuma yi wa wadanda suke makoki ta’aziyya.
A wani labarin kuma, Rikicin Siyasa: An Kama Mutane 60 Bayan Kona Motoci 3, Da Jikkata Wasu da Dama a Kano
Biyo bayan rikicin da ya barke tsakanin magoya bayan jam’iyyun siyasa masu hamayya da juna a hanyar Zaria dake jihar Kano, akalla mutane 63 da ake zargi jami’an tsaron farin kaya na Najeriya NSCDC ne suka kama.
Magoya bayan jam’iyyar da ke hamayya da juna sun yi amfani da muggan makamai a yayin arangamar da suka hada da kona motoci uku tare da farfasa wata guda inda aka tabbatar da jikkata wasu da dama.