Daga: Abbas Yakubu Yaura
Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya mika ta’aziyya ga iyalan tsohon firaministan kasar Japan Shinzo Abe.
Shugaban ya kuma jajanta wa gwamnati da jama’ar Japan game da kisan Abe.
KARANTA WANNAN LABARIN: https://dimokuradiyya.com.ng/wata-tirela-ta-murkushe-mutane-8-raguna-sallah-a-jihar-kwara/
An harbe dan siyasar da safiyar Juma’a a lokacin da yake gabatar da jawabi gabanin zaben ‘yan majalisar dokokin da za a yi ranar Lahadi.
Buhari ya bayyana firaministan kasar Japan da ya fi dadewa kan karagar mulki a matsayin fitaccen shugaba, inda ya ba da tabbacin addu’o’i da tunanin daukacin ‘yan Najeriya.
Ya ce za a tuna da Abe bisa jajircewarsa na karfafa kasuwanci da saka hannun jari a tsakanin Afirka da Japan ta hanyoyi daban-daban.
Shugaban ya tuna cewa Abe ya yi amfani da kayan aikin Tokyo International Conference on African Development (TICAD) don haɗin gwiwa.
“A karkashin Abe, Najeriya da Japan sun ji daɗin haɗin gwiwa mai mahimmanci, suna tallafawa burin juna game da haɗin gwiwar tattalin arziki, kiwon lafiya, haɓaka albarkatun ɗan adam, rage haɗarin bala’i, zaman lafiya da tsaro”, in ji shi.
Buhari ya yi addu’ar Allah ya sa tunawa da marigayin ya zama alheri ga al’ummarsa, “wadanda ya yi wa hidima da sadaukarwa”.
A wani labarin kuma Ɗan Takarar Shugaban Ƙasa a Jam’iyyar NNPP, Sanata Rabi’u Musa Kwankwaso a ranar Alhamis yace dukkanin Jam’iyyu biyu na APC da PDP, sun kasa, sai yayi kira ga Al’umma a Jahar Osun da su zaɓi Jam’iyyar NNPP a zaɓen Gwamna na ranar 16 ga watan juli.
A cewar sa, ƙudirin NNPP na karɓe Najeriya ya fara daga Osun, a yayin da dukkanin manyan Jam’iyyu na Ƙasa basu da abinda zasu iya yi. Ya bukaci masoyan sa, dasu zama a shirye a kowane lokaci domin zaɓar Ɗan Takarar Jam’iyyar a lokacin zaben Gwamna.
Kwankwaso, wanda yayi jawabi a Osogbo a taron da NNPP ta shirya, domin gangamin yaƙin neman zaɓe na Ɗan Takarar ta a Osun, Dr Oyelami Saliu, Yayi kira ga masu rajistar Katin Zaɓe da basu karba ba, suje su karɓa, tare marawa Jam’iyyar baya a lokacin zaɓen.
Yace “ƴaƴan Jam’iyyar mu da dama a shirye suke su zaɓi Ɗan Takarar Gwamna na Jam’iyyar mu dake zuwa.
“Magoya bayan mu naso su ga sabuwar Najeriya daga Osun. Tsarin Jam’iyyar mu shine haɗin kai, ba tare da kula ta Ɓangaran ci, Addini a wannan ƙasar. Waɗanda basu karbi Katin Zaɓe suje su karɓa, sannan su zaɓi Jam’iyyar mu.
“Ƙasa zaɓar Jam’iyyar mu domin kawo cigaba mai ma’ana, na nufin baiwa wadancan damar cigaba da mulkar mu. Dukkanin mu, mun san wadannan Jam’iyyun sun kasa mana, kuma babu abinda zasu bada. Mu kore su kawai, kuma wannan ya fara ne daga wannan Jahar.