Mejo Janar Mayirenso Saraso, Kwamandan Sashen 2 na rundunar hadin gwiwa ta shiyyar Arewa maso Gabas, Operation HADIN KAI (OPHK), ya nemi goyon bayan shugabannin gargajiya na jihar Yobe wajen magance tashe-tashen hankula.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da kaftin Kennedy Anyanwu, mataimakin daraktan hulda da jama’a na rundunar soji ta 2 OPHK, ya fitar ranar Juma’a a Damaturu.
KARANTA WANNAN LABARIN: Xi Jinping Ya Shiga Tarihi A Matsayin Shugaban Kasar China Mai Wa’adi Na Uku
A cewar sanarwar, Saraso ya ziyarci Dr Bashir Bukar, Sarkin Nguru, Alhaji Mustapha Mai-Kyari.
Wani sarkin da ya ziyarta shi ne na Bade, Alhaji Abubakar Suleiman, wanda kuma shi ne mataimakin shugaban majalisar sarakunan jihar Yobe.
Saraso ya ce an kai ziyarar ne domin yin rijistar kasancewar sa, da girmama shi, neman albarkar sarki da jagoranci daga masarautun.
Ya ce ziyarar ta zo daidai da al’adar sojojin Najeriya.
Ya kuma bukaci karin goyon baya daga sarakunan kasar musamman ta fuskar musayar bayanai da kuma bayanan sirri, inda ya nuna cewa hakan zai samar da kyakkyawar alaka tsakanin sojoji da jama’a a jihar.
Sanarwar ta ce, sarakunan sun gode wa kwamandan sashin da mukarrabansa bisa wannan ziyarar da suka kai masa, tare da ba shi tabbacin bayar da goyon bayan da zai samar da zaman lafiya, inganta harkokin tattalin arziki da ci gaban jihar.
Sarakunan sun yi wa kwamandan da dakarun sa addu’o’in samun nasarar gudanar da ziyarar aiki a jihar.
A cewar sanarwar, Saraso ya kuma kai ziyarar gani da ido na sansanonin sojoji da sassan da ke karkashinsa.
Kazalika ya ziyarci Bataliyar Nguru ta 241, Bataliya ta 159 Gashua da kuma daya daga cikin wuraren da rundunar ke aiki a Kanama.
Yayin da yake jawabi ga hafsoshi da sojoji a wurare daban-daban, ya bukace su da su ci gaba da kasancewa cikin siyasa, da’a da sadaukar da kai wajen gudanar da ayyukan da aka ba su. (NAN)
A wani labarin kuma, An Gurfanar da Tsohon Firaministan Malaysia a Gaban Kotu
Tsohon firaministan Malaysia Muhyiddin Yassin a ranar Juma’a ya gurfana gaban kotu bisa tuhumarsa da laifin yin amfani da karfin ikonsa na karbar cin hanci da kuma karkatar da kudade da ke da nasaba da zargin yin amfani da asusun farfado da tattalin arzikin kasar na COVID-19.
Muhyiddin ya kasance Firaminista na tsawon watanni 17 tsakanin shekarar 2020 zuwa 2021, a daidai lokacin da Malaysia ke yakar cutar corona, kuma yanzu yana jagorantar kawancen adawa da gwamnatin Firaminista Anwar Ibrahim. shugaba Najib Razak, wanda a halin yanzu yake zaman gidan yari na shekaru 12 saboda rawar da ya taka a badakalar kudi a asusun saka hannun jari na jihar 1MDB.