Dakarun Habasha dana Sudan sun yi arangama a yankin Al-Fashaga da ake takaddama a kai, bayan tsintar gawarwakin sojojin Sudan bakwai da wani farar hula da aka kashe a karshen makon jiya..
Kana a ranar Talata Sudan ta bayyana cewa ta kwato wasu sassan kasarta da sojojin Habasha ke rike da su.
A halin da ake ciki kuma, yankin al-Fashaga na yankin arewa maso yammacin Amhara na kasar Habasha ne, wanda ya hade da yankin Breadbasket na jihar Gedaref na kasar Sudan.
Kazalika rahotanni daga kasashen biyu na nuna cewa, an shafe shekaru sama da goma ana gwabzawa fada tsakanin kasashen biyu kan yankin, yayin da wutar rikicin takara zafafa tun farkon shekarar data gabata.
A wani labarin kuma na daban.
Rundunar Soji zata yi amfani da Tsaffin Sojoji domin magance matsalar tsaro
Rundunar Sojin Ƙasa zata cigaba da amfani da Tsofaffin Sojoji wajen magance matsalar tsaro a ƙasar, kamar yadda Shugaban Sojojin Ƙasa Laftanar-Janar Faruk Yahaya ya bayyana.
Yahaya ya bayyana haka a ranar Talata da daddare a wata liyafar cin abinci daya shirya ga Jami’an Soji da suka ajiye aiki a Shekarar 2021 daga Division na 3, Rukuba, Kusa da Jos.
Shugaban Sojin wanda ya samu wakilcin Shugaban Barikin kuma Shugaban Shirin Operation Safe Haven Manjo-Janar Ibrahim Ali, ya godema Jami’an Sojin da sadaukarwar su, da Jajircewa a lokacin da suna aiki.
Ya bayyana cewa irin ƙwarewar da tsofaffin Sojojin suka nuna ana buƙatar shi wajen cigaban Rundunar Sojin Ƙasa a kokarin ta na magance matsalolin tsaro a Kasar.
“Akwai wani yunƙuri da muke yi domin amfani da Tsaffin Sojoji dake da gogewa ta aiki, domin ya zama dole wajen magance matsalolin tsaro na Ƙasar mu,” Inji shi.
Yahaya ya ƙara dacewa,wannan liyafar cin abinci da aka shirya masu, an yi ta ne domin yabawa da irin aikin da suka yiwa Ƙasar su.
Shugaban Sojin ya yi kira ga Jami’an Soji da suke aiki a halin yanzu da suka ƙoƙari wajen tsare martaba da kima ta Ƙasa, yana mai shan alwashin baiwa jindadin su fifiko.