Wani Malamin addinin Musulunci Mai suna Malam Ma’adawa, ya bayyana cewa, tallafa wa matasa wajen ci gaba da ilimi da kuma sana’o’in dogaro da kai ne mafita, da za su kawo karshen matsalolin tsaro da ke addabar Nijeriya. Malamin dai ya shahara wajen bayar da gudummowarasa a kan abubuwan da dama da suka shafi ci gaban matasa tare da gyara halayensu a zantawarsa da wakilinmu da ke Zariya, ya bayar da shawarwar kan matakan tsaro day a kamata gwamnatoci su dauka, domin kawo karshen matsalolin tsaro da suke neman durkusar da al’ummar Nijeriya da kuma Nijeriyar kanta. Malam Ibrahim Ma’adawa ya ci gaba da cewar, in an dubi yadda ake samun matasa a gungun aikata muggan ayyuka, da suka hada da kungiyoyin da ake alakanta shi da addini ko kabilaci da kisar gilla ga al’umma da kuma garkuwa da mutane, duk, kamar yadda fitaccen malamin ya ce, matasa ke kan gaba a cikin ayarin da suke aikata muggan ayyukan da aka ambata. A kan haka ne Malam Ma’adawa ya tunatar da gwamnatin tarayya da kuma musamman gwamnatin jihar Kaduna, da su cika alkawurran da suka yi kafin zaben shekara ta 2015, cewar, in sun sami nasara za su farfado da masana’antun da suka durkushe a sassan Nijeriya, musamman a jihar Kaduna. Ya kara da cewar, kanfar ayyukan yi ga matasan Nijeriya da kuma tsadar ci gaba da karatu a makarantun gaba da sakandare na kan gaba da ya shafi matsalolin da suka sa matasa ba su iya ci gaba da neman ilimi a makarantu da kuma jami’o’in da suke Nijeriya. Malam Ibrahim Ma’adawa, ya kuma tunatar da gwamnatin jihar Kaduna, musamman gwamna Malam Nasir Ahmed El- Rufa’i, na alkawarin farfado da kamfanonin jihar Kaduna da suka durkushe, da suka hada da` na allurar asibiti da ke Zariya da kamfanin citta da ke garin Kaciya da kamfanin tumatir da ke garin Ikara da kuma kamfanin rake da ke garin Makarfi, wadannan kamfanoni da aka ambata, a cewar fitaccen malamin a shekara hudu da suka gabata, babu daya da gwamnatin jihar Kaduna ta dora dambar gyaransa, sai dai batun shirin gyaran a kafafen watsa labarai, in ji shi. Game kuma da zaben wannan shekara ta 2019, Malam Ibrahim Ma’adawa ya nunar da cewar, duk wanda ya lura da yadda zaben ya kasance, ya san an yi zabe lafiya, in an dubi yadda al’umma suke ta batun cewar, za a iya samun tashin hankali a lokutan wadannan zabubbuka, wannan ya faru ne, in ji Malam Ma’adawa, a dalilin tashi tsaye da aka yi da ya shafi jan kunnuwar matasa kan illolin bangar siyasa da fadace-fadace a lokutan zabe. Malam ya kuma tunatar da gwamnatoci cewar, tun da matasa sun jib shawarwarin da aka ba su, da kuma jan kunnuwar da aka yi ma su, to ya dace zababbu su fara fitowa da wasu tsare-tsare da za su tallafa wa rayuwar matasan Nijeriya. Sai dai kuma a zantawar da wakilinmu ya yi da Malam Ma’adawa, ya nuna matukar damuwarsa da yadda wasu malamai suka aje nauyin da aka dora ma su, na fadin gaskiya kamar yadda mai kowa mao komi ya ce su yi, sai kawai suka jefa kansu a cikin siyasa tsundum, wannan, kamar yadda ya ce, babban kuskure ne da ya kamata wadannan malamai su gyara tafiyarsu, domin mutuncinsu ya ci gaba da zama a idon al’umma, kamar yadda ake kallonsu a baya.