Tsohon Sakataren Gwamnatin tarayya, Babacir Lawal ya ce Bola Ahmed Tinubu ne ya taka gagarumar rawa wajen tarawa shugaban kasa Buhari kudin yakin neman zaben da ya taimaka masa samun nasarar zaben shekarar 2015.
A wata hirar da ya yi da Jaridar Punch, Babacir ya ce Buhari da magoya bayansa ba su da kudin da za su iya taimaka masa lashe zabe, sai dai manufofi da kuma goyan bayan da suke da ita a hannun wasu ‘yan Nijeriya.
Tsohon Sakataren Gwamnatin ya ce Tinubu ya yi amfani da ‘yan kasuwar da ya sani wajen tara makudan kudaden da Buhari ya yi amfani da su wajen kayar da shugaba Goodluck Jonathan a zaben da aka yi.
Babacir ya ce daga cikin wadanda suka bada gudummawa har da wasu dake kusa da gwamnatin Jonathan saboda yadda suka gamsu da tabbacin da Tinubu ya gabatar musu.
Tsohon Sakataren Gwamnatin ya ce shi da ministan man fetur Timipre Sylva sun yi iya bakin kokarinsu wajen ganin sun samawa Buhari kudaden yakin neman zabe amma sai suka gaza, har sai da Tinubu ya sanya hannu.
Babacir ya ce bayan kudaden tallafi da Tinubu ya samawa Buhari, ya yi kuma amfani da dukiyarsa wajen yakin neman zaben da kuma dauko hayar wadanda suka taimakawa tsohon shugaban Amurka Barack Obama yakin neman zabe wajen tallata shugaba Buhari.
Tsohon Sakataren ya ce shigowar wadancan mutane daga Amurka ya sa Buhari ya fara bayyana da kayan Yarbawa da Igbo da Kanuri, kana ya fara bayyana a hotuna tare da iyalansa.
Babacir ya ce a lokacin ne kuma aka fara fito da Uwargidansa Aisha Buhari tana halartar tarurruka da kuma jawabi domin nema masa goyan baya.