Wakilinmu shu’aibu Ibrahim Gusau
Tsohon shugaban kasa Yakubu gawon ya kawowa gwamnan jihar zamfara, Hon. Bello Muhammad Matawalle, ziyara ta musamman domin tayashi murna da yiwa jihar zamfara da kasa baki daya addu’a ta musamman.
Da yake gabatar da jawabinsa tsahon shugaban kasan Yakubu Gawon, ya ce karkashin kungiyarsa Wadda take yi wa kasa addu’a, sun zo jihar zamfara domin su taimaka mata da addu’a na musamman, domin ko ba komai jihar zamfara tana butakar addu’oi saboda halin da ta Sami kanta a ciki na rashin tsaro, Wanda yace wannan wani shirine da suka kirkira nayiwa kasa addu’a da jimawa.
Gawon, ya bayyana cewa yau da gobe zasu gabatar da addu’oi a coci sannan su gabatar da zagaye, Kuma za’a gabatar da wadannan addu’o’in ne tare da musulmi na wannan jihar.
Da yake maida jawabinshi gwamnan jihar zamfara, Hon. Bello muhammad matawallen ya bayyana cewa wannan ziyarar ya zo dai dai lokacin da jihar zamfara take bukata, domin a cewarsa babu abinda take bukata Kamar addu’a.
Gwamnan ya Kara da cewa sakamakon addu’oi da akeyi ya Sanya Shirin da gwamnati ta fito da shi na sulhu da barayi ya Soma samun nasara.
Matawallen na maradun, ya ce zuwa yanzu an Sami nasarar karbar bindigogi guda 247, daga hannun maharan, yace nan bada jimawa ba zamfara zata tsinci kanta cikin jihohi masu zaman lafiya.
Gwamnan ya bayyana cewa shi da kanshi ko kuma wasu daga cikin jami’an gwamnati zasu halarci cocin da za’a gudanar da addu’oin na musamman.
Matawallen, ya tabbatarwa Gawon, cewa gwamnatinsa ta kowa da kowa ce, Kuma zata samarwa kiristocin jihar zamfara da wasu mukamai ta Basu, domin yace sun taka rawar gani wajan kafuwar gwamnatinsa.