Wajibi ne mu Himmatu wajen kare Hakkin ‘ya’ya Mata a Najeriya, duba da irin yadda ake cin zarafin ‘ya’ya Mata a kasar nan musamman kananan yara da masu ciki uwa Uba Ma’aurata yadda zaka ga mutum ya sami matarsa ya rika duka tamkar an kawo masa wata Jaka alhali abin da ya hadasu shine So da kaunar Juna.
Kuma lokacin da zai zo neman Aurenta bai taba nu na mata cewa shi dan damben gargajiya ne da zai rika gwada kwanjinsa a kanta ba hasali ma nu na mata yayi cewa shi din nan mutumin kirki ne hakan tasa har ta amince da shi to yanzu dan me zai rika wulakanta ta yana mata yadda yaso ba tare da tausayawa ba.
mu mata a kowana lokaci mun fi bukatar lallashi da tausayi maimakon gwada karfi na lura da wani abu mafi yawan matsalolin da ake kawo wa gabanmu na fyade zaka ga daga cin amana ne sai ‘yan kalilan da ba zamu rasa ba na gwada karfi, amma mafi yawan matsalolin fyade na cin amana ne, don haka mu a kungiyar Rigar Yanci International muka fito da wani shiri mai suna Mu Hana Fyade, shiri ne wanda yake zagayawa lungu da sako wajen Ilimantar da iyaye mata yadda zasu kula da ‘ya’yansu a lokuta kamar irin in zasu fita unguwa ya ya zasu yi da yaransu kuma wajen wa ya kamata su bar ‘ya’yan nasu.
Idan fita unguwa ta kamasu kuma wace yarinya ce ake aikanta kasuwa ko shagon kofar Gida balle ma wani lokaci sai ka ga wasu iyayen sun bar yaransu wajen wani gardi da sunan dan uwansu ko kuma wani wanda suke girmamawa shi kuma karshe sai ki ga yayi amfani da wannan damar wajen yiwa ‘yarki fyade.
Don haka muka ce iyaye mata ku mu fito mu yaki masu irin wannan mugunyar dabi’a a cikin al’ummarmu kazalika tilas ne duk matar kirki ta yiwa mijinta biyayya kamar yadda addinin musulunci ya tanadar ba irin yadda zaki ga wasu mazan sun maida matansu ababen bukatarsu ba, ma’ana mace tana da kima da mutunci ne kawai idan suka nemi bukatarsu da ita suna gamawa kuma shi kenan bata da sauran kima.
To irin wadannan mazaje Allah na fushi dasu da ayyukansu domin babu abin da ya hada musulunci da wannan aikin ta’addancin nasu musulunci yayi Gabas su kuma sun yi yamma, amma da zaran an tashi sai kaji sun bude baki suna fadin Matayenku Gonakinku ne lallai haka yake a musulunce, amma musulunci yayi cikakken bayani game da ma’anar gonakinku da kuma irin fahimtar da mazan yanzu suke ma wannan ayar fassara.
Mutumin da musulunci ya ce cinta, da shanta, da wajen kwananta , kula da lafiyarta, suturarta, duk sun doru a kanshi amma sai yaki yi, kuma ya ce wannan matar gonarsa ce, to tambaya? Shin kin daukar wancan nauyin da yayi shi kuma ya sunan shi maza nake tambaya? Domin babu addinin da ya kammala kamala ta cika irin musulunci dan haka sai da yayi bayanin komai a fili ba a boye ba.
Dan haka maza ya kamata ku gane mata raunana ne kuma ababen tausayawa saboda haka muke son mu kawo karshen Cin Zarafin ‘ya’ya mata a kasar nan da duniya baki daya, kuma zamu samu nasaran yin hakan ne da taimakon masu madafan iko, Alhamdulillah yanzu gwamnatin tarayya tayi doka mai tsanani ga duk wanda aka samu yayi fyade ba zargi ba sannan muna kira ga ‘yan majalisar tarayyar Najeriya da su yi wata doka da zata rika hukunta maza masu dukan matansu ko masu hana matansu abinci alhali yana aiki kuma ana biyansa amma da zaran ya karbi albashin shi to shi kenan ita da ganin sa sai bayan ya cinye komai zata ganshi .
don haka yasa muke kira ga hukumomi da su rika taimakawa iyayenmu mata a duk lokacin da bukatar hakan ta taso mu kuma iyayen yara mu tabbatar muna kula da yaranmu yadda ya kamata tun kama daga kawayensu zuwa wuraren da suke mu’amala da irin hirarrakin da ke fitowa daga bakunansu in suna Magana a waya ko a fili ke uwa ya kamata ki sani ‘yarki itace mutuncin ki in ta rushe ke ma kin rushe, sannan duk matar da ta bari ‘yarta tana fita yadda taga dama sannan bata san komai game da ita ba kuma in aka ga wani abu game da ‘yar aka sanar da ita sai kaji ta ce ba komai Allah zai shirya, lallai Allah ne mai shiriya amma ke ma da kanki kina da gudummawar da zaki bada wajen tarbiyar ‘yarki da kanki ai Hausawa na cewa Allah ya ce tashi in taimake ka kinga kuwa in kika zauna ai zaki ga zama.
Sannan wannan kungiya tamu a shirye take ta kwatowa mata hakkin su a ko’ina yake a fadin duniya sannan muna koyar da mata sana’o’in hannu daban-daban a wannan kungiya mai albarka ta Rigar Yanci International kuma a shirye muke mu bada kowacce irin gudummawa ga ‘ya’ya mata domin karesu daga dukkan wani farmaki ta ko’ina a fa]in duniya.