By Abbas Yakubu Yaura
Wasu fursunoni uku sun tsere daga gidan yarin Mandala na Hukumar Kula da gidan gyaran halin ta Najeriya (NCoS) a Ilorin dake jihar Kwara.
Wadanda suka tsere, a cewar rahoton da Premium Times ta wallafa, an bayyana sunayensu da Umaru Altine, wanda aka yankewa hukuncin kisa da laifin fashi da makami; da Segun Nasiru da kuma Isa Usman, dukkansu ana tuhumar su da laifin fashi da makami da kuma jiran shari’a.
“Sun tsere a farkon alhamis bayan sun yanke ƙarfe dakin da suke,” in ji jaridar, tana yin la’akari da sadarwa na ciki na NCoS game da ci gaba.
Da yake magana da manema labarai ciki harda jaridar Dimokuradiyya a ranar Lahadin da ta gabata, mai magana da yawun NCoS, Francis Enobore, ya ce ana ci gaba da gudanar da bincike kan lamarin.