Naniya Suleiman, ya yi korafi kan cinkoso da ake fama da ita a gidan yarin inda ya ce an tsara gidan yarin ne domin mutum 500 amma yanzu akwai fursunoni 947.
Ya ce: “Mafi yawancin su kotun shari’a ce ta yanke musu hukuncin kisa. Akwai wasu kuma da ake yanke wa hukuncin datse hannaye ko kafafuwa amma suna zaune a gidan yari fiye da shekaru 10 ba tare da sannin matsayin su ba.
Ba a datse hannun su ba, ba a datse kafafuwan su ba, ba su san matsayar su ba. “Akwai wadanda aka yanke wa hukuncin kisa ta hanyar jifa. Lamarin yana damu na.
“Zuciya ta tana sosuwa duk lokacin da na kai ziyara gidajen yarin domin sukan taso su tambaye ni halin da suke ciki.
“Na rubuta wasika ga gwamna da Alkalin Alkalai na jiha domin neman a dauki mataki a kan su.
“Ba za a iya kai su kotu ba saboda an yanke musu hukunci sai dai ba a zartas da hukuncin ba.
Shugaban na gidan yarin ya ce idan ba za a iya zartas musu da hukuncin ba ana iya sauya hukuncin su zuwa zaman gidan yari.
Idan hakan ba zai yiwu ba, sai ayi musu afuwa a kuma basu horro na sauya halaye sannan a sake su.
Ina bukatar gwamnati ta zartas da hukuncin idan kuma hakan ba zai yiwu ba doka ta bawa gwamna ikon yi musu afuwa.”
A cewar Majalisar Dinkin Duniya zartar da hukuncin kisa cin zarafi ne na bil adama.