Yadda Ƴan Sanda Suka Yi Awon Gaba Da Ƴan Fashin Jigawa 7 A Jigawa
Rundunar ‘yan sandan jihar Jigawa ta ce ta kama wasu barayi bakwai da wani mai gadin makaranta bisa laifin satar kadarorin makarantar.
A cikin wata sanarwa da kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Lawan Shiisu Adam ya fitar, ya ce, “A ranar 14/9/2023 da misalin karfe 5, jami’an sa ido na sashen Kiyawa sun kama wani Aminu Abdullahi mai shekaru 30 a kauyen Balagu da ke karamar hukumar Kiyawa da wata saniya da ake zargin an sace ta.
KARANTA WANNAN LABARIN:NLC ta fara fuskantar turjiya daga wasu ƙungiyoyi kan tsunduma yajin aiki
“Da ake yi masa tambayoyi, wanda ake zargin ya bayyana cewa kimanin wata daya da ya wuce ya je kauyen Kudai da ke karamar hukumar Dutse domin yin aiki a gonar wani Baba Haruna, kuma a hanyarsa ta komawa gida sai ya ga wannan saniya a bayan gida daya ya yanke shawarar sace ta. An gano mai saniyar kuma ya gano saniyarsa.”
Ya kara da cewa an kama wasu mutane shida da ake zargin barayin ne a sassa daban-daban na jihar.
Game da mai gadin makarantar, Shiisu ya ce, “A ranar 19 ga Satumba, 2023, wani Bashir Ahmed ‘m’ shekaru 50, mataimakin shugaban makarantar sakandiren ‘yan mata ta gwamnati, Kazaure, ya kawo rahoto a sashin Kazaure cewa a ranar 18/9/2023 da misalin karfe 18/9/2023 5 , ya gano cewa an sace wasu kadarorin makarantar.
“Bayan samun rahoton, jami’an sa ido na sashen Kazaure sun dira a wani shago da ke Kan Gada Kazaure, inda wani mai suna Hassan Adamu mai shekaru 30 a kauyen Bornu-Kishi, jihar Yobe, wanda jami’in tsaro ne a yankin, an kama shi da buhu biyu masu dauke da abubuwa kamar haka: injin buga takardu, kwamfutoci guda biyu, fanin silin guda biyu da na’urar daukar hoto.
“Lokacin da ake yi masa tambayoyi, wanda ake zargin ya amsa cewa ya yi amfani da babban mabudin bude kantin sayar da kayan kuma ya kwashe kayan makarantar.
A wani labarin kuma:Kotu ta daure Matashin da ya yiwa budurwa fyaɗe shekaru 5
Wata kotun majistare a jihar Kwara ta daure wani mutum mai suna Tashiu Aminu Lulu shekaru biyar a gidan yari bisa samunsa da laifin yi wa wata budurwa ‘yar shekara 18 fyade.
Tun da farko dai an kama wanda ake zargin ne biyo bayan koken da wanda aka yiwa fyaɗen ta kai ga hukumar tsaro ta farin kaya (NSCDC) reshen Kaiama.