Wata dusar kankara ta lalata gonaki da gidaje a al’umomin Dutsen-Kura da Kanya da Gozaki a karamar hukumar Kafur ta jihar Katsina.
Dimokuradiyya ta rawaito cewa, Malam Abdullahi Gozaki, wani mazaunin garin Gozaki ya shaida wa Daily trust cewa babu wanda ya taba ganin faruwar irin wannan abu a yankin.
Ya ce ta lalata filayen noma da rufin gidaje da gilashin mota sakamakon dusar kankarar da ta dauki tsahon mintuna kadan.
Karanta kuma: Dusar Kankara Ta Hana Tashin Jiragen Sama A Istanbul
Ya lissafa al’ummar da abin ya shafa kamar su Gidan Danwada, Gidan Sabo, Kabalawa, Unguwar Tsamiya, Dandabo, Unguwar Maigarma, Unguwar Wanzamai da Unguwar Fulani.
Da yake tsokaci kan lamarin, shugaban karamar hukumar Kafur, Alhaji Garba Kanya, ya ce dusar kankarar ta lalata gonaki fiye da 300 a wasu al’ummomi da ke yankunan da lamarin ya shafa.
Ya ce ta lalata amfanin gona da dama na miliyoyin naira da suka hada da masara, gero, shinkafa, waken soya, albasa da barkono, inda ya kara da cewa “a wasu gonaki, shinkafa da aka kusa girbiwa.”
Ya kara da cewa an sanar da hukumomin da abin ya shafa da suka hada da Hukumar Noma da Raya Karkara ta Jihar Katsina (KTARDA) da Hukumar Ba da agajin gaggawa ta jihar (SEMA) kuma sun yi nazari kan irin barnar da ta yi.
A wani labarin kuma: Yajin Aikin ASUU: Yadda Matafiya Suka Makale Ya Yin Da Dalibai Suka Rufe Hanya
Matafiya sun makale a kan titin Legas zuwa Ibadan yayin da daliban da ke zanga-zangar yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ke ci gaba da yi suka tare hanyar a ranar Talatar nan.
Daruruwan Dalibai a karkashin kungiyar dalibai ta kasa (NANS) sun dakatar da zirga-zirgar ababen hawa.