Kotun sauraren kararrakin zaben gwamna dake zaune a garin Ibadan a ranar Litinin ta yi watsi da karar da dan takarar gwamna a jam’iyyar APC, Adebayo Adelabu ya shigar yana mai kalubalantar zaben gwamnan PDP a Oyo da sunan bai cancanci tsayawa takara ba.
Adelabu wanda yake shi ne tsohon mataimakin gwamnan Bankin Nijeriya, CBN yana dai kalubalantar zaben gwamna Seyi Makinde na watan Maris din 2019.
Shugaban kwamitin da ke sauraren karar, Sirajo Muhammed a hukuncin da ya yanke a ranar Litinin, ya tabbatar da cewa mai shigar da karar Cif Bayo Adelabu na APC ya kasa gabatar da gamsassun hujjoji da suke tabbatar da zarginsa wanda ya sabawa dokokin zabe na 2010.
Da yake maida martani, daya daga cikin Lauyoyin da ke bai wa Adelabu kariya, Akin Olujimi, ya ce za su hadu da sauran lauyoyi masu mukamin SAN’s domin nazarin hukuncin kotun. Inda ya ce daga nan ne za su san matakin da ya kamata su dauka.