Shugaban jami’ar jihar Benue BSU dake Makurdi, Farfesa Joe Iorapuu, ya bayyana cewa yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta shiga na tsawon watanni shida a fadin kasar nan, tuni ya yi illa ga kwakwalwar dalibai.
Iorapuu ya bayyana hakan ne a lokacin da yake amsa tambayoyi daga wasu ‘yan jarida a Makurdi a ranar Alhamis kan makomar daliban da suka kammala karatun digiri bayan yajin aikin ASUU da aka tsawaita.
KARANTA WANNAN LABARIN: Ambaliyar Ruwa: Gwamnatin Kano Ta Fara Rusa Haramtattun Gine-gine A Kasuwa Kantin Kwari
Ya ce daliban sun dade suna zama a gida har abin ya shafi hankalin su, ya ce akwai bukatar malamai masu yajin aiki su fadada tunaninsu ta hanyar yin watsi da ayyukansu.
“Ko (yajin aikin) zai shafi daliban; ya riga ya shafi tunanin dalibai. Akwai sabuwar tattaunawa game da lafiyar hankali; tuni ya shafi daliban.”
“Yata guda da ya, ya kamata ta kammala kusan shekara guda yanzu tana rataye a Jami’ar Jos saboda duk wadannan abubuwa. Biyu daga cikinsu akwai; wanda yake a matakin aji 100 yakamata ya kasance a matakin aji 300 yanzu.
“Don haka, ka ga mu ma muna fama da wadannan (yajin aikin). Yana ba ni zafi cewa yaranmu suna fama da cutar tabin hankalin. Mu ma wadanda abubuwan ya shafe mu kuma al’umma wani lokacin ba ta fahimta. Shi ya sa nake cewa mu (abokan aiki) mu zauna mu sake tunani,” inji shi.
Mataimakin shugaban jami’ar ya jaddada bukatar gwamnatin tarayya da na jihohi su dauki ilimi da muhimmanci a lokacin da suke shirye-shiryen kasar nan domin kawo karshen yajin aikin na dindindin a fannin ilimi.
A wani labarin kuma, ‘Yan Awaren Tigray Na Zargin Gwamnatin Habasha Kai Musu Munanan Hare-Hare
Kwana daya kafin nan, gwamnatin Habasha ta ce ‘yan kabilar Tigray na fadada fadan da ake gwabzawa a kan iyakokin kasar da Sudan.
Tun da farko, An kasashen duniya sun sha yin kiraye-kirayen kawo karshen sabon rikicin da ya balle a kasar..