By Abbas Yakubu Yaura
Wasu da ake kyautata zaton ‘yan bindiga ne sun kai hari kauyen Rijiya dake karamar hukumar Gusau a jihar Zamfara, inda suka kashe mutane shida tare da yin garkuwa da wasu da dama.
Wani mazaunin kauyen mai suna Musa Sani da ya gudu zuwa garin Gusau yace ‘yan bindigar dake kan babura sun zo kauyen ne da misalin karfe 1:30 na rana a ranar Lahadi inda suka fara harbin mutane.Ya kara da cewa yana can a wani bangare na kauyen sai ya ji karar harbe-harbe da kururuwar mutanen kauyen, wadanda ke ta ihun neman agaji. Hakan ya sa ya gudu daji domin tsira da rayuwar sa.Sannan yace na yi gaggawar gudu zuwa wata gona dake kusa inda na buya har barayin suka bar kauyen.
“Lokacin da suka bar kauyen, mun gano cewa sun harbe mutane shida tare da raunata wasu da dama.
“Sun kuma yi garkuwa da mata da yara da dama wadanda har yanzu ba a tantance adadinsu ba. Na yanke shawarar barin kauyen zuwa Gusau saboda tsoron kada ‘yan fashi su dawo domin ba wannan ne karon farko da wadannan miyagu ke kai mana hari ba.
Munyi kokarin jin ta bakin Kakakin rundunar ‘yan sandan jihar, Mohammed Shehu, sai bai amsa kiran muba har zuwa lokacin hada wannan rahoton.
A halin da ake ciki, jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa ‘yan bindiga suna ci gaba da kai hare-hare ga al’ummar jihar duk da matakan tsaro da gwamnatin jihar ta dauka na dakile wannan ta’asa.
Manoman da dama sun yi watsi da gonakinsu, kuma sun kasa girbe amfanin gonakinsu, sakamakon hare-haren da ‘yan fashin ke kaiwa.kazalika, kauyuka da dama sun zama ba kowa, yayin da ’yan gudun hijira da dama suka koma garin Gusau inda suka nemi abinci da mafaka.