Wasu ‘yan bindiga da ake kyautata zaton masu garkuwa da mutane ne sun yi garkuwa da basaraken al’ummar Isuokoma mai cin gashin kansa a karamar hukumar Onicha ta jihar Ebonyi, Eze Ambrose Ogbu.
Jaridar PUNCH ta ruwaito wasu da har yanzu ba a tantance ko su waye ba sun yi awon gaba da sarkin ne a daren ranar Laraba a fadarsa da ke Isu a yankin karamar hukumar.
Wata majiya mai tushe da kuma masu ruwa da tsaki a cikin al’ummar da ta nemi a sakaya sunanta ta tabbatar da faruwar lamarin ga wakilin majiyar jaridar Dimokuradiyya a Abakaliki a ranar Alhamis.
A cewar majiyar, wadanda suka yi garkuwa da mahaifin sarkin ba su tuntubi danginzsa ba har zuwa lokacin hada wannan rahoton, ranar Alhamis da yamma.
“An yi garkuwa da shi a daren jiya a fadarsa. Amma masu garkuwa da mutanen ba su yi kira dangi ko kuma jama’a a waya ba. Mun kasance muna jira haryanzu; amma har yanzu ba a tuntube su ba,” inji majiyar.
Rundunar ‘yan sandan jihar Ebonyi, a ranar Alhamis ta tabbatar da faruwar lamarin.
Kwamishinan ‘yan sanda na jihar, Aliyu Garba, a wata tattaunawa da ya yi da wakilin jaridar PUNCh, a Abakaliki, ya ce ‘yan bindigar sun yi wa gidan mahaifinsa kwanton bauna, a daren ranar Laraba, inda suka yi awon gaba da shi.
Yayin da yake tabbatar da cewa wadanda suka yi garkuwa da sarkin ba su tuntubi iyalansa da hukumomi ba, shugaban ‘yan sandan ya ce jami’an rundunar sun gaggauta daukar matakin ganin basaraken ya sake haduwa da iyalansa.