Majalisar wakilan Tarayyar Najeriya, ta yi Allah wadai da kisa da satar mutane a Arewa maso yammacin kasar nan, Inda suka ba da goron gayyata ga Shugaba Muhammad Buhari.
Dan majalisar Safana, ne ya kawo kudurin inda aka tafka muhawara, kan garuruwan da Abin ya Shafa kamar irin su Kasai, Alhazawa, Guzurawa, da kuma Gobirawa, a Jihar katsina, inda maharan sukayi amfani da bindiga kirar AK47 kan babura Sama da 200.
A Garin Safana, da Batsari, cikin Awa 48, an Kashe Mutane Sama da 12 kuma anyi asarar gidaje da dukiyoyi Masu Dimbin Yawa.
Wanda hakan ya nuna gazawar Gwamnatin Tarayya ga yadda abubuwa ke faruwa a yankin inda mata da kananan yara ke watangaririya a Matsayin ‘Yan Gudun Hijirah wasu kuma Marayu.
Dubi Harin baya bayan nan kuma kullum abin sai karuwa yake ana kashe Wanda basuji ba ba su gani ba satar mata da kone wurare Abin Hauhawa ya ke Kullu Yaumin.
Kowace gwamnati babban aikin ta shine kula da rayuwa da dukiyar kasa, Inda ya koka kan jami’an tsaro da cewa basuyi wani abun azo a gani ba.
Shugaban Kwamitin Majalisar mai lura da doka da kasuwanci Edward Pwajok, na Jam’iyyar APC daga Jihar Filato, yace Najeriya ta samu matsala kan yadda kisa yake da da yaduwa ko wacce rana.
Mataimakin Shugaban Majalisar Yusuf Lasun daga APC Dan Jihar Osun, ya kara da cewa rashin daukan Kwakkwaran mataki kan makasan da Wanda suke aikatawa hakan yasa Lamarin ke ci Tamkar Wutar Daji.
Bashir Babale na APC daga Jihar Kano, yace duk yadda jami’an tsaro ke kokarin dakile Ayyukan ‘Yan Ta’adda a kasar nan, amma har Yanzu yankin Arewa Yana cikin Jerin Matattarar kisa da satar mutane.
A Nashi Bangaren Chika Adamu na APC daga Jihar Neja, cewa yayi jami’an tsaro basu da kwarin gwiwa Duba da yadda manyan sojoji suke tsoron bin hanyar Abuja zuwa kaduna.
Gabriel Onyewife na Jam’iyyar PDP ya Zargi manyan gwamnati yadda suka Rasa karsashin tunkarar matsalar nan ta tsaro.
Abiante Dagimie, na PDP daga Jihar Ribas, ya ce in har dai gwamnati da gaske take to lokaci yayi da zata dau mataki kan satar mutane da yawan Kashe-Kashe a Najeriya.