Jami’an Rundunar Yan sanda na kasa na gudanar da bincike kan fille kan wani dan majalisar wakilai a jihar Anambra da ke kudu maso gabashin kasar nan, mako guda bayan da wasu ‘yan bindiga suka yi garkuwa da shi tare da wani mataimakisa.
An gano gawar Okechukwu Okoye da aka yankewa Kai ne a karshen mako jiya, inda ya haifar da fargaba.
A lokacin da yake mayar da martani Gwamnan jihar Anambra Charles Soludo ya bayyana kisan a matsayin abin ban tsoro, dabbanci da ban tsoro.
Kana ya Kuma sanar da bayar da tukuicin Makudan kudade ga duk wanda ya bayar da bayanan da za su kai ga kama wadanda suka yi kisan duk da cewa ba a san ko su waye suka kai harin ba.
Jami’ai sun zargi haramtacciyar kungiyar ‘yan aware da karuwar tashe-tashen hankula a yankin.
Masu fafutukar kafa kasar Biafra da ke fafutukar neman ballewa daga kasar nan, sun musanta hannu a hare-haren na baya bayan nan.
Sai dai kuma shugabanta Nnamdi Kanu na fuskantar shari’a kan ta’addanci da cin amanar kasa wanda ya musanta aikata wadannan laifuka