Rundunar ‘yan sandan Nasarawa ta ce ta cafke wasu mutane uku da ake zargi’ yan kungiyar asiri ne wadanda ke tayar da hankulan mazauna karamar hukumar Akwanga ta jihar.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan, ASP Ramhan Nansel, ne ya bayyana hakan, yayin da yake zantawa da wakilin jàridar Dimokuradiyya a jiya Asabar a Lafiya.
Ya bayyana cewa, wadanda ake zargin ‘yan kungiyar asiri ne, karkashin jagorancin wani Mai suna Timothy Ishaya, dan shekara 21, suna cikin jerin wadanda da ake nema ruwa-a-jallo saboda yawan ta’addanci da hargitsa zaman lafiyar mazauna yankin.
Kakakin ‘yan sandan ya kara da cewa, “An sami gatari guda daya, busasshen ganyen da ake zagin Tabar Wi-Wi ne, wuyan hannu guda biyu, masu adon sihiri da dais auran su.”
KARANTA WANNAN LABARIN: Kungiyar NUPEG za ta tsunduma yajin Aiki Gobe
ASP Nansel ya ce an gurfanar da wadanda ake zargi a gaban kotu.
A wani Labarin Kuma na daban
Mista Mohammed Idris, Shugaban Majalisar Karamar Hukumar Nassarawa Eggon ta Jihar Nasarawa, ya bayyana kaduwarsa kan harin da aka kai wa Waziri Umbugadu Enwongulu, mai ba da shawara kan sha’anin APC na mazabar Wakama.
Yace harin tare da kona gidan na Mista Paul Angbazo, babban dan uwana kuma jigon na APC, bai dace ba kuma basa da tsoron Allah.
Idris ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin da yake yin ta’aziyya tare da wanda aka kashe a Wakama, Karamar Hukumar Nassarawa Eggon.Shugaban karamar hukumar, wanda mataimakinsa, Mista Ben Manga ya wakilta, ya bayyana lamarin a matsayin abin takaici da dabbanci.
“Ban san dalilin da yasa wasu mutane ba sa son zaman lafiya ba, Me za su samu yanzu da suka rushe wannan gida. “Muna kira ga mazauna Wakama dasu kwantar da hankulansu, su kasance masu bin doka domin jami’an tsaro za su zakulo wadanda suka aikata laifin.
Shi ma da yake jawabi, Messrs Thomas Bawa, Shugaban masu ruwa da tsaki na jam’iyar APC,da unguwar Wakama, Litinin Nanza, Garba Adigizi da Akolo David, da sauran manyan jiga -jigan jam’iyyar, sun yi Allah wadai da harin baki daya.
Sun bukaci hukumomin tsaro dasu kamo wadanda suka aikata munanan ayyukan tare da tabbatar da hukunta su daidai da dokokin da suka dace.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa a ranar 7 ga watan Oktoba, Hukumar zabe mai zaman kanta ta Jihar Nasarawa ta bayyana cewa jam’iyar APC ta lashe dukkan shugabanci kujeru 13 da mukaman kansiloli 147 a zaben kananan hukumomi da aka gudanar a ranar 6 ga watan Oktoba.
Comments 1