Rundunar ‘yan sanda a jihar Delta ta ce ta kashe wasu mutane uku da ake zargin ‘yan fashi da makami ne tare da kama daya, a wasu hare-hare biyu na fashi da makami a jihar.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar, DSP Bright Edafe, a wata sanarwa da ya raba wa manema labarai jiya a Warri, ya ce jami’an ‘yan sandan da ke aiki da sashin Ozoro da ke yankin Isoko ta Arewa da kuma shiyya ta Orogun a Ughelli ne suka harbe mutanen uku a ranar Alhamis. A karmar Kananan Hukumomin dake jihar.
Majiyar Jaridar Dimokuradiyya ta ruwaito Edafe ya ce an kwato bindigogi guda uku da aka kera a cikin gida, harsashi mai kisa da babur daya, ya kara da cewa tuni rundunar ta fara bincike kan lamarin.
(NAN).
A wani labarin kuma na daban.
Shehu Sani, tsohon dan majalisar tarayya, ya ce ya kamata a bi dokoki da ka’idoji da aka shimfida wajen maye gurbin Alkalin Alkalan Najeriya CJN.
Sani ya bayyana haka ne biyo bayan rahotannin da ke cewa Mai shari’a Tanko Muhammad ya ajiye mukaminsa na alkalin alkalan Najeriya.
A wani sako da ya wallafa a shafinsa na Twitter a ranar Litinin, Sani ya rubuta cewa: “Ya kamata wanda zai maye gurbin CJN ya bi ka’idojin da aka gindaya. Bai kamata a yi tsalle-tsalle ba domin a samu wanda zai dace da siyasa, bangaranci, addini ko kabilanci na masu mulki.”
A baya Jaridar Dimokuradiyya ta ruwaito cewa Muhammad ya yi murabus ne a daren Lahadin da ta gabata, saboda rashin lafiya da ya sa ya yanke hukuncin.
Har sai da ya yi murabus, rahotanni sun nuna cewa Mai Shari’a Muhammad na fama da matsanancin rashin lafiya.
Muhammad ya kasance mai shari’a a kotun kolin Najeriya tun shekarar 2005 kuma an nada shi a matsayin alkalin alkalan Najeriya a shekarar 2019.
Ya taba zama Alkalin Kotun daukaka kara ta Najeriya.