An sako wani fitaccen dan siyasar Sudan daga gidan yari kwana guda gabanin kawancen farar hula da ya ke da shi ya rattaba hannu kan wata yarjejeniya ta farko da sojoji domin kawo karshen takaddamar siyasa da ya haifar da juyin mulkin watan Oktoban 2021.
Dan siyasar Wagdi Salih, wanda aka sake shi ranar Lahadi a ofishin ‘yan sanda a Khartoum babban birnin kasar, yana kan gaba a kwamitin yaki da cin hanci da rashawa da aka kafa bayan hambarar da tsohon shugaban Sudan Omar al-Bashir a shekara ta 2019.
KU KARANTA: Rayuwata Na Cikin Hatsari Saboda Fallasa Karerayin Dake Cikin Takardun Gwamna Mai Ci, Jigon PDP
Kwamitin da aka dorawa alhakin rusa gwamnatin Al-Bashir, ya fuskanci suka daga janar-janar da ke raba madafun iko da farar hula na ‘yanci da sauyi (FFC) kafin su gudanar da mulkinsu, tare da dakatar da mika mulki da ke da nufin kai ga zaben dimokuradiyya.
An saki Salih ne tare da wani dan sanda da ya yi aiki a kwamitin.
Hadaddiyar kungiyar sa ta FFC ta kira kama shi a watan Oktoba da “siyasa ce kawai”.
Sudan dai ta kasance ba tare da firaminista ba tun bayan juyin mulkin, kuma tattalin arzikinta da ya riga ya shiga cikin mawuyacin hali ya durkushe bayan da aka dakatar da biliyoyin daloli na taimakon kudi na kasa da kasa.
Sojoji da FFC sun sanar a ranar Juma’a cewa suna da niyyar rattaba hannu kan wata yarjejeniya, tare da wasu kungiyoyi, don mika mulki karkashin jagorancin farar hula da za a fara bayan kulla yarjejeniyar karshe.
Majalisar Dinkin Duniya, Amurka, Saudiyya, da Hadaddiyar Daular Larabawa ne suka dauki nauyin tattaunawar.
Wannan dai ba shi ne karon farko da hukumomi ke kama Salih ba.
A watan Fabrairu, jami’an tsaro sun tilasta masa daure shi a babban birnin kasar, Khartoum.
A wani labarin kuma: Dole ‘Yan Najeriya Su Hukunta APC Ta Hanyar Hana Ta Kuri’u A 2023 – Atiku
Dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar PDP, Atiku Abubakar, ya bukaci ‘yan Najeriya da su hukunta jam’iyyar APC, ta hanyar hana ta kuri’u a zaben 2023 mai zuwa.
Atiku ya yi wannan roko ne a wata wasika ta musamman da ya aikewa magoya bayansa ta email, ranar Lahadi.
Ya bayyana cewa idan kasa ta kasance mai girma, dole ne ta kasance a hade tare da hadewa. Kuma idan kasa ta kasance mai hadin kai, dole ne ta mallaki shugabancin da ke shirye ya yi aiki bisa manufa.