Rundunar ‘yan sandan jihar Adamawa ta ce, ta cafke wasu mutane shida da ake zargi masu garkuwa da mutane ne da suka kai hari ofishin’ yan sanda na Ngurore da ke Yola ta Kudu, kuma suka yi garkuwa da wata uwa.
Kamfanin Dillancin Labaran Kasa NAN ya ruwaito cewa, lamarin ya faru ne a ranar 10 ga watan Oktoban shekarar nan, kuma an ceto wadanda abin ya shafa.
Kwamishinan ‘yan sandan jihar, Mista Mohammed Barde ne ya bayyana hakan, yayin wata ziyarar ban girma da kwamitin hulda da jama’a na‘ yan sandan Adamawa (PCRC) ya Kai shalkwatar rundunar a yau Alhamis a garin Yola Babban Birnin jihar.
Ya ce rundunar a shirye take don magance duk wani aiyukan garkuwa da mutane, fashi da makami, da sauran ayyukan laifi fadin jihar.
KARANTA WANNAN LABARIN: Tabbas an Farmaki Jirgin Abuja zuwa Kaduna~NRC
Barde ya yi kira da a ci gaba da ba kwamitin goyon baya ta hanyar ba da bayanai masu amfani ga ‘yan sanda, don tabbatar da zaman lafiya da tsaro a fadin kananan hukumomi 21 na jihar.
Ya ba su tabbacin cewa za a tafiyar dda irin wadannan bayanai cikin sirri.
Kwamishinan ya shawarci Kwamitin na PCRC da su ci gaba da kasance wa masu hadin kai, wajen gudanar da ayyukansu da kuma wasu bangarori daban -daban.
Mista Olu Adegoke, Shugaban Kwamitin PCRC na Jiha, ya ba Barde tabbacin cikakken goyon baya da haɗin kai don tunkarar ƙalubalen tsaro a jihar.
A wani labarin Kuma na daban
Shugaban Ƙungiyar Ƴan Aware na tsagerun IPOB Nnamdi Kanu yace bai aikata laifun da ake zargin shi ba, wanda Gwamnatin Tarayya ta sake yin kwaskwari ma ga wata ƙara data shigar a kanshi.
A yau ne ya bayyana a gaban kotun Babbar Birnin Tarayya Abuja, akan ƙarar shi da akeyi na zagon ƙasa, da ta’addanci, wanda Gwamnatin Tarayya ta sake yin kwaskwari ma akan haka, ga ƙararraki guda bakwai da ake zargin shi da aikatawa.
Jim kaɗan bayan ya bayyana cewar bashi da laifi a yau, Babban Jojin ya bada umarnin a cigaba da tsare shi a kurkukun Hukumar Jami’an tsaron farin ta DSS, bayan anƙi yarda da buƙatar shi na mayar dashi a cibiyar gyaran aƙida.
An ɗage zama shari’ar zuwa 10 ga watan Nuwamba na Shekarar 2021