By Abbas Yakubu Yaura
Gwamnatin Tarayya ta ayyana hawan jirgin kasa kyauta ga ‘yan kasa daga ranar 24 ga watan Disamba, 2021 zuwa 4 ga watan Janairu, 2022.
Manajan daraktan hukumar kula da layin dogo ta Najeriya Fidet Okhiria ne ya bayyana hakan a wata hira da yayi da kamfanin dillancin labarai na Najeriya ranar Juma’a a Abuja.
Ya ce, “Shawarar da aka yanke tare da haɗin gwiwar ma’aikatar sufuri, ita ce sauƙaƙe zirga-zirgar ga ‘yan ƙasa a lokacin yuletide.
“Wannan shine don taimakawa wajen sauƙaƙe farashin sufuri da kuma baiwa ‘yan ƙasa damar motsawa cikin sauƙi don jin daɗin lokacin bukukuwa.
Sai dai an shawarci fasinjoji da su tabbatar sun samu tikitin daga wuraren da suka dace ba tare da farashi ba, don ba su damar shiga cikin jiragen.
“An kuma umurci dukkan fasinjoji dasu kiyaye tare da yin biyayya ga dokokin COVID-19 ta hanyar sanya abin rufe fuska, wankewa da tsaftace hannu. “
Ya kuma nanata kudirin gwamnatin tarayya na tabbatar da tsaron fasinjoji da jiragen kasa a lokacin.