Masu kaɗa ƙuri’a a Mazaɓa ta 13, Akwati na 002, sunyi zanga-zanga akan rashin aikin da Na’urar Tantance masu zaɓe take yi, da aka turo a Akwatin.
Majiya tace babu wani mai kaɗa ƙuri’a da aka tantance a Akwatin, tunda safe sabudda matsalar Na’urar.
Ɗan takarar Jam’iyar APGA Farfesa Chukuma Soludo har yanzu baiyi zaɓe ba, sabudda matsalar da Na’urar ta haifar.
KARANTA WANNAN LABARIN: Ƴan uwan Shugaba Buhari sun jinjina wa Gwamna Yahaya akan biyayyar sa, sun buƙace shi ya fito takara a 2023
A akwati na 001 na Isuofia majiyoyi sunce an fara zaɓe da misalin karfe 9:21, amma da wakilin Jaridar Dimokuraɗiyya yaje wurin ya tarar mutum 15 kaɗai suka kaɗa ƙuri’a.
Haka zalika, a Akwati na 005 na Isuofia, masu kaɗa ƙuri’a sun nuna damuwa akan yadda tun bayan da jami’an INEC suka fara tantace masu kaɗa ƙuri’a daga misalin ƙarfe 9:12 na safe, masu kaɗa ƙuri’a 20 ne kaɗai suka samu nasarar jefa ƙuri’ar su har zuwa ƙarfe 11:00 dai-dai.
Wani tsoho Mr Udoka Okafor ya shaida cewa bai gamsu da yadda ake gudanar da zaɓen ba.
Yace duk da INEC tasha alwashin cewa ta shirya gudanar da zaɓen, amma abunda ke damuwa a yanzu abun baƙin ciki ne.
Yace “ina nan tun ƙarfe 9:30 na safe, amma har yanzu ban kaɗa ƙuri’a ba.
Na’urar Tantance zaɓen taƙi tantance ni, amma dole inyi abinda yake haƙƙina.