Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya ce ba ya da wanda ya fi so cikin Yan takara, gabanin zaben fidda gwani na Yan takarar shugaban kasa na jam’iyyar APC Mai mulki
Buhari ya kuma shaida wa Gwamnonin Arewa da ke Aso Rock da suka gana da shi kan inda ya kamata Shugaban kasa ya fito domin su ba wa wakilai damar yanke shawara. Dole ne jam’iyyar ta shiga zaben fidda gwani, babu wanda zai nada kowa.”
Shugaban a ranar Litinin da yamma ya ce yana da muhimmanci a share duk wani shakku game da inda ya tsaya kan zaben dan takarar shugaban kasa.
Buhari, a cewar Garba Shehu, ya bayyana hakan ne a gaban gwamnonin jam’iyyar 14 na jihohin Arewa.
A cewar shugaban, “babu wanda aka fi so,” kuma bai “shafawa kowa ba Kai ba,” kuma ya kuduri aniyar tabbatar da cewa “ba za a sanya wani dan takara a jam’iyyar ba.”
Buhari ya ce jam’iyyar tana da muhimmanci kuma dole ne a mutunta mambobinta, kuma a ji su na da muhimmanci.
Shugaban ya ce ya na da hankali kan abin da yake yi don haka ya nemi gwamnonin APC su ji haka.
A halin da ake ciki kuma, rahotanni sun bayyana a ranar Litinin cewa shugaban jam’iyya mai mulki na kasa, Abdullahi Adamu ya zabi shugaban majalisar dattawa Ahmad Lawan a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar.
Sai dai mambobin kwamitin zastaswa na kasa (NWC) na jam’iyyar APC sun musanta amincewa da shugaban majalisar dattawa, Ahmad Lawan a matsayin dan takarar shugaban kasa na jam’iyyar.