Rundunar ’yan sandan Nijeriya ta yi zargin cewa wasu ’yan siyasa da ba ta ambato sunayensu ba su na horar da ’yan dabar siyasa tare da ba su makamai gabanin zaben gwamna da za a gudanar a ranan 16 ga watan Nuwambar wannan shekara.
Wakilin babban sufeton ’yan sandan Nijeriya, Muhammed Adamu, wanda kuma shi ne mukaddashin babban sufeto (DIG) mai kula da aikace-aikace a hedikwatar rundunar ta kasa da ke Abuja, DIG Abdulmalik, ne ya bayyana hakan a Lokoja.
Alhaji Abdulmalik ya ja kunnen duk wanda ke shirin tayar da zaune tsaye da ya shiga taitayinsa, domin a cewarsa, rundunar ’yan sandan ta shirya tsaf domin tabbatar da ganin an gudanar da zaben gwamnan cikin kwanciyar hankali da lumana a jihar ta Kogi.
Har ila yau ya ce, babu wanda ya fi karfin doka, inda ya ce, duk wanda a ka kama ya na kokarin karya doka, zai yaba wa aya zakinta.
DIG Abdulmalik ya cigaba da cewa binciken rundunar ’yan sanda ta kasa ya nuna cewa wasu jam’iyyun siyasa su na nan su na horarwa tare da samarwa da ’yan daban siyasa makamai domin tada fitina a ranar zaben gwamnan jihar Kogi da za a gudanar a ranar 16 ga Nuwambar wannan shekara.
A kan haka ne ya gargadi masu neman haddasa hayaniya da su guji yin hakan, inda ya nanata da cewa duk wanda a ka kama zai dandana kudarsa komai matsayinsa.
DIG Abdulmalik ya kuma ce rundunar ’yan sandan ta kasa za ta turo ’yan sanda fiye da 25,000 zuwa jihar Kogi domin ganin an samar da isasshen tsaro Kafin, lokaci da kuma bayan zaben gwamnan.
Abdulmalik, wanda ya wakilci shugaban ’yan sandan Nijeriya, ya zo lokoja ne domin halartar taron masu ruwa da tsaki da shugaban hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC), Farfesa Mahmud Yakubu, ya kuma bada tabbacin cewa rundunar ’yan sandan Nijeriya za ta sauke nauyin dake kanta na tsaron lafiya da kuma dukiyoyin jama’a a dukkan matakai.
A sabili da haka nema yayi kira ga jama’ar jihar ta Kogi, musamman ’yan siyasa da su guji dukkan abubuwan da ka iya kawo rashin zaman lafiya kafin, lokaci da kuma bayan zaben, inda a karshe ya jaddada cewa, “idan kunne ya ji, gangar jiki yta tsira”.