By Abbas Yakubu Yaura
Hukumar Zabe Mai Zaman Kanta ta Kasa (INEC) ta sanar da dakatar da ci gaba da rijistar masu kada kuri’a a babban birnin tarayya Abuja (FCT) gabanin zaben kananan hukumomin da za a gudanar a yankin.
Kwamishinan INEC na kasa kuma shugaban kwamitin yada labarai da wayar da kan masu zabe, Barista Festus Okoye ya bayyana hakan a wata sanarwa daya fitar ranar Alhamis a Abuja.
Wani bangare na sanarwar yana cewa; “A cikin sashe na 103 (1) na dokar zabe ta shekarar 2010 (kamar yadda aka gyara), hukumar ta ba da ikon gudanar da zabuka a ofisoshin shugaban kasa, mataimakin shugaban kasa, da ‘yan majalisun kananan hukumomin babban birnin tarayya (FCT).
“A bisa ga wannan ikon, hukumar ta yi taro a ranar 30 ga watan Maris, 2021, ta kuma sanya ranar Asabar 12 ga watan Fabrairu na shekarar 2022 domin gudanar da zaben wadannan mukamai.
“A cikin sashe na 9 (5) na dokar zabe ta shekarar 2010 (kamar yadda aka gyara),yin rajistar masu kada kuri’a,da sabunta rajistar masu kada kuri’a,sannan da mai mai ta rijistar masu kada kuri’a zasu tsaya nan da kwanaki 60 kafin gudanar da duk wani zabe da dokar ta shafa.
“Saboda haka, Hukumar, bisa bin ka’ida, za ta dakatar da yin rajistar masu kada kuri’a a babban birnin tarayya Abuja daga ranar 12 ga watan Disamba, 2021.
“Don shawo kan tashe-tashen hankulan da ake sa ran yin rajistar masu kada kuri’a ta (CVR) a babban birnin tarayya Abuja, hukumar ta tura karin na’urorin tantance masu kada kuri’a (IVED) zuwa cibiyoyin rajistar, inda aka raba jimlar IVED guda 17 inda ake bayar da guda 2 ga kowace karamar hukuma da 5 a Cibiyar Rajista.
“Dukkanin alƙawuran da suka wuce 12 ga watan Disamba na shekarar 2021 an sake tsara su kuma an aika da sanarwa ga waɗanda abin ya shafa ta imel.
“Hukumar ta kuma dakatar da ayyuka na duk sabuntar masu kada kuri’a, canja wuri, da sake dubawa dangane da birnin tarayya FCT.
“Za a buga katunan zabe na dindindin (PVCs) na sabbin masu rajista kuma za a ba su damar karba nan da nan bayan an kammala ayyukan da ake bukata da kuma gabanin zaben da aka shirya yi ranar Asabar 12 ga watan Fabrairu na shekarar 2022.
Jaridar Dimokuradiyya ta rawaito cewa “Hukumar tace zata ci gaba da jajircewa wajen ganin an gudanar da zabe cikin gaskiya da adalci a Najeriya.”