Zaben gwamnan jihar Osun, hukumar zabe mai zaman kanta ta kasa (INEC) ta fara rabon muhimman kayayyaki ga daukacin kananan hukumomi 30 na jihar.
Jami’an INEC sun kwashe kayan cikin tsauraran matakan tsaro a daren Alhamis a shedkwatar hukumar da ke kan titin Gbongan/Osogbo.
A lokacin da yake raba kayan, kwamishinan zabe na jihar Osun, Farfesa Abdulganiy Raji ya ce jami’an zabe za su kai kayan cibiyoyi inda za a tura su rumfunan zabe a Asabar din nan.
A cewar sa, an dauki wannan matakin ne domin tabbatar da isar da kayayyakin yadda ya kamata zuwa rumfunan zabe ranar Asabar.
A cikin dabarun da suke da shi na kara kaimi a zaben, jam’iyyun da ke da rinjaye kamar – (APC), Labour Party (LP) da jam’iyyar (PDP) – duk sun gudanar da babban taro da su domin jan hankalin masu zabe su kada kuri’a gare su.
Yayin da tsohon mataimakin kakakin majalisar wakilai, Yusuff Lasun shine dan takarar jam’iyyar LP, ita kuma jam’iyyar PDP ta tsayar da Sanata Ademola Adeleke a matsayin dan takararta tare da gwamna mai ci Gboyega Oyetola na neman sake tsayawa takara a karkashin jam’iyyar (APC).
Duk mutanen biyu za a zubar a ranar Asabar din nan a jihar Osun tare da yanke shawarar wanda zai mulke su na tsawon shekaru hudu masu zuwa.