Sakataren jamiyyar APC na kasa Iyiola Omisore ya musanta zargin da ake cewa wasu sunyi amfani da kudi wajen siyan kuri’u, a yayin zaben jihar Osun wanda ake gudanar da shi a yau Asabar.
Omisore ya musanta hakan ne bayan ya kammala kada kuri’ar sa a akwatin Moore mai Lamba 003, dake Ile Ife, a karamar hukumar Ife ta gabas dake jihar ta Osun.
Ya dai isa zuwa wajen kada kuria’ar ne da misalign karfe 10:30 na rana, ya bayyana farin cikinsa dangane da yadda mutane suka fito don kada kuri’a, kuma ya yaba da irin yadda jamiyyar su ta APC ke ci gaba da samun tagomashi.
Da yake ganawa da manema labarai, kuma suka tambaye shi dangane batun zargin siyan kuri’a ya musanta batun cewa ana siyan,inda ya bayar da misali cewa shi da idonsa baga wani waje da hakan ta faru ba.
Daga nan sai ya bukaci hukumar INEC kan ta kara himma wajen kyautata tsarin amfani da na’urar tantancewa da aka samar, wadda a cewarsa tana cike da kalubale, wajen tantance wadanda suka kamata ace an tantance su.
A karshe ya bayyana fatan sa na ganin jamiyyar su ta samu nasarar lashe zaben baki daya, wanda yace suna da irin wannan fatan a babban zaben dake tafe.