Zamu ɗauki tsatstsauran Mataki ga wanda suke bayan Matsalar Tsaron Najeriya — Buhari
Shugaban Ƙasa Muhammadu Buhari a ranar Alhamis a Kano yace Gwamnatin sa zata ɗauki tsatstsauran Mataki dake haifar da Tsoro da Matsalar Tsaron Najeriya.
KARANTA WANNAN LABARIN: Ƴan Sanda sun hallaka Ƴan bindiga 4, sun kama matar da take Saida Makamai a Kaduna
Shugaban yayi kira ga Sabbi da Jami’ai na Rundunar Ƴan Sandan Najeriya dasu ƙara azama domin cigaba da tsaron Ƙasar akan ƴan ta’adda wanda suke so kullum ƴan ƙasa su kasance cikin tsoro.
Dayake jawabi a lokacin bikin yaye Ƴan Sanda na Makantar Horas da Ƴan Sanda ta Wudil Kano, Shugaba Buhari yace Gwamnatin sa nayin aiki tuƙuru da Tattalin Arzikin ta domin ganin ta sanya Rundunar Ƴan Sandan Najeriya “daga cikin jami’an tsaro Masu ƙarfi a faɗin Duniya.”
Babban Mai Taimakawa Shugaban Ƙasa akan Kafafen Yaɗa Labaru Garba Shehu, ya bayyana haka a cikin wata sanarwa daya fitar a ranar Alhamis mai taken “mun cimma nasarori ta fuskar tsaro, Tattalin Arziki, Cin Hanci, inji Shugaba Buhari, sai ya buƙaci ƴan sanda dasu aiki da Fasahar zamani’.
Dayake bada jawabi akan yaki da Matsalar Tsaro, Buhari yace Ƴan Boko Haram, da Ƴan IPOB, da Ƴan Bindiga a wasu sassan Ƙasar, an rage masu karfi sosai, kumi tuni zaman lafiya ya dawo a wasu garuruwa da ƙauye.
Comments 1