- Kotun sauraren kararrakin zabe ta Majalisar Dattawa da ke zamanta a Umuahia ta kori ‘yan majalisar wakilai uku da aka zaba jam’iyyar LP
- Hakan ya biyo bayan wata kara da dan takarar jam’iyyar APC ya shigar a gabanta
- Kotun ta lura cewa an ayyana dan takarar jam’iyyar LP cikin kuskure don haka ba zai iya tsayawa ba
Kotun sauraren kararrakin zabe ta Majalisar Dattawa da ke zamanta a Umuahia, babban birnin jihar Abia a ranar Litinin ta kori ‘yan majalisar wakilai uku da aka zaba a karkashin jam’iyyar Labour, Punch ta rawaito.
Wani kwamitin kotun da ke karkashin jagorancin mai shari’a Adeyinka Aderibigbe ya kori dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Arochukwu/Ohafia, Mista Ibe Okwara Osunwa, bisa rashin bin dokar zabe ta 2022.
Hakan ya biyo bayan wata kara da dan takarar jam’iyyar APC ya shigar a gabanta Daniel Okeke.
KARANTA WANNAN: Da Dumi-Dumi: IGP ya Kafa Kwamitin Ba da Lasisin Mallakar Bindiga
Kotun ta umarci hukumar zabe mai zaman kanta da ta janye takardar shaidar cin zabe da aka baiwa Osunwa tare da bawa Okeke wata sabuwar takardar.
A wani labarin kuma, wani kwamitin da mai shari’a Hajaratu Hajjo Lawa ta jagoranta ya soke zaben Munachim Alozie, mai wakiltar mazabar tarayya ta Obingwa/Osisioma/Ugwunagbo.
Kotun ta kuma bayar da umarnin sake gudanar da zabe cikin kwanaki 90 masu zuwa kamar yadda kundin tsarin mulkin kasar ya tanada.
Kotun ta lura cewa an ayyana dan takarar LP cikin kuskure don haka ba zai iya tsayawa ba.
Da yake karanta hukuncin, Farfesa Muhammad Mahmud a madadin kwamitin mutum uku da Lawal ya jagoranta, ya ce adadin masu kada kuri’a ya zarce adadin wadanda suka kada kuri’a a wasu rumfunan zabe da suka karbi katin zabe na dindindin.
Dan takarar jam’iyyar YPP, Ibe Michael Nwoke, ya garzaya kotun ne bayan bayyana Alozie a matsayin wanda ya lashe zaben majalisar dokokin kasar da aka gudanar a ranar 25 ga watan Fabrairu inda ya bukaci a soke shi.
Nwoke ya roki kotun da wasu abubuwa da ta soke zaben LP na Alozie saboda ba a zabe shi da kyau ba kuma zaben sa ya kasance marar inganci bisa la’akari da rata.
Yayin da lauyan dan takarar YPP aka yanke hukuncin a matsayin adalci, lauyan LP ya dage kan daukaka karar.
Hakazalika, wani kwamitin kotun ya soke zaben dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Aba ta Arewa da na tarayya ta kudu Mista Emeka Nnamani, kan takardar shaidar jabu.
Kotun ta bayyana dan takarar jam’iyyar APGA a zaben, Alex Ikwueche a matsayin wanda ya lashe zaben sannan ta umurci INEC da ta janye takardar shaidar cin zabe da aka baiwa Nnamani sannan ta ba Ikwueche wata sabuwa.
A wani labarin kuma, Indiya ta mika wa Brazil shugabancin G20
Indiya ta mika wa Brazil shugabancin G20 a hukumance a bikin rufe taron shekara-shekara da aka yi a New Delhi a karshen mako.
Firayim Ministan Indiya Narendra Modi ya kammala mika mulki ne ta hanyar mika ragamar shugabancin ga shugaban kasar Brazil Luiz Inacio Lula da Silva.