- Hukumar EFCC, ta jaddada kudirinta na kin barin cin hanci da rashawa ya ci gaba da lalata zamantakewar al’ummar Najeriya
- Ya Kamata al’umma su hada kai don ganin an dakile cin hanci da rashawa da ta bayyana a matsayin dodo mai kaifi a cikin kasar
- Dole ne mu tashi tsaye, mu inganta gaskiya, tare da karfafa cibiyoyinmu idan har za a dakile wannan barazana da ake kira cin hanci da rashawa
Hukumar yaki da masu yi wa tattalin arzikin kasa zagon kasa, EFCC, ta jaddada kudirinta na kin barin cin hanci da rashawa ya ci gaba da lalata zamantakewar al’ummar Najeriya.
Don haka ta yi kira ga al’umma da su hada kai don ganin an dakile cin hanci da rashawa da ta bayyana a matsayin dodo mai kaifi a cikin kasar.
KARANTA WANNAN: Kotu Ta Baiwa Tsohon AGF, Adoke Izinin Tafiya Kasar Waje
Da yake jawabi a yayin wani tattaki a garin Uyo, babban birnin jihar Akwa Ibom, domin murnar zagayowar ranar yaki da cin hanci da rashawa ta duniya na shekarar 2023 mai taken, “UNCAC @20: Hadin Kan Duniya Kan Cin Hanci da Rashawa,” Kwamandan Shiyya na EFCC, ACE-1 Bawa Hamidu Saidu ya yi nuni da cewa, idan har za a shawo kan cin hanci da rashawa, ya kamata jama’a su hada kai, su inganta gaskiya, da tabbatar da karfafa cibiyoyi.
A cewarsa: “Dole ne mu tashi tsaye, mu inganta gaskiya, tare da karfafa cibiyoyinmu idan har za a dakile wannan barazana da ake kira cin hanci da rashawa. Ba za mu iya barin cin hanci da rashawa ya kara ruguza kasar nan ba, mun tsaya a matsayin jama’a a kan cin hanci da rashawa, mun kayar da cin hanci da rashawa! Kuma mun hada kai, mun dauki wurin da ya dace.”
Kwamandan shiyyar ya kuma bayyana cewa, wajen hada kan kungiyar yaki da cin hanci da rashawa ta duniya, shiyyar za ta yi aiki ba tare da barin tsangwama ba, sannan kuma da tabbatar da cewa an kira masu cin hanci da rashawa ba tare da la’akari da matsayinsu na zamantakewa ba.
“A Najeriya a yau, cin hanci da rashawa ya sa mu fuskanci alkibla, ko da kuwa alkiblar da za mu bi, tana kawo cikas ga kowane bangare na ci gabanmu da dorewar muhalli tare da yin illa ga marasa galihu a cikin al’umma.
“A shirye mu ke mu kira masu cin hanci da rashawa ko kungiyoyi, na sirri ko na jama’a, ba tare da la’akari da sanin wane ne gora ba, dole ne mu hada kai wajen yaki da cin hanci da rashawa, mu yi hakan ba tare da tsangwama ko ga addini, jam’iyyar siyasa, kabilanci ba ko kuma akida, ka yi tunanin duniyar da ta hada kai da gaske wajen yaki da cin hanci da rashawa,” in ji Saidu.
A wani labarin kuma, Da Dumi-Dumi: CBN Ya Gargadi ‘Yan Najeriya Kan Yadda Ake Yada Jabun Kudaden Naira
Yayin da Najeriya ke fama da karancin kudi, babban bankin Najeriya ya gargadi ‘yan Najeriya game da yada jabun takardun kudin Naira
Tuni CBN ya ba da tabbacin cewa yana aiki da jami’an tsaro domin kamo masu laifin
Duk wanda aka Kama da aikata laifin zai Fuskanci hukuncin zaman gidan yari na shekaru 5
Yayin da Najeriya ke fama da karancin kudi, babban bankin Najeriya ya gargadi ‘yan Najeriya game da yada jabun takardun kudin Naira.
A ranar Juma’a ne babban bankin ya bayar da wannan gargadin a cikin wata sanarwa mai taken ‘Hattara da jabun takardun kudin Naira da ke kewayawa Cikin al’umma’.