- Hukumar Kwastam ta Najeriya reshen jihar Sokoto ta mika katan 1,198 na magungunan jabu ga hukumar NAFDAC dake Sokoto
- Magungunan da ba a yi wa rijista ba suna da matukar hadari ga al’ummar kasa
- Hukumar ta ta gargadi masu fasa-kwauri da su daina wannan aika-aika domin rundunar a shirye take don dakile wannan aika-aika
Hukumar Kwastam ta Najeriya reshen jihar Sokoto, a ranar Laraba, ta mika katan 1,198 na magungunan jabu ga hukumar kula da ingancin abinci da magunguna ta kasa dake Sokoto.
Da yake jawabi yayin mika kayayyakin ga hukumar a ofishin shiyya na Sokoto, Kwanturola Musa Omale, ya ce kwacen ya yi daidai da manufar hadin gwiwa da babban Kwanturola Janar na Kwastam Bashir Adewale Adeniyi ya yi.
KARANTA WANNAN: Neja: An ceto Mutane 11, Takwas Sun Mutu, Wasu Sun Bace A Hatsarin kwale-kwale
Ya jaddada cewa magungunan da ba a yi wa rijista ba suna da matukar hadari ga al’ummar kasar, inda ya ce matsalar jabun magungunan annoba ce ta duniya da duniya ke fama da ita.
Ya kuma baiwa hukumar ta NAFDAC tabbacin goyon bayan rundunar kan yaki da jabun magunguna.
Sai dai ya gargadi masu fasa-kwauri da su daina wannan aika-aika domin rundunar a shirye take don dakile wannan aika-aika.
Ya ce, “Don sarrafawa, ba a yarda da shigo da Magungunan ta kan iyakar ƙasar nan ba.
“Sabis ɗin ya daidaita shigo da duk Magunguna ta hanyar tashar jiragen ruwa da aka keɓe, kuma ana share su ne kawai bayan cika takaddun da ake buƙata.”
Magungunan da aka mika sun hada da Katon 450 na Real Extra Tablet, fakiti 405 na magungunan inganta jima’i, katon 148 na kwaroron roba, katan 30 na magungunan Vernos da ake taunawa, da sauransu.
Ko’odinetan NAFDAC na Sokoto, Garba Adamu, ya godewa hukumar bisa hadin kai da hadin gwiwa wajen kare rayuka da lafiyar ‘yan Najeriya.
A wani labarin kuma, Kotun Daukaka Kara Ta Tsige Ɗan Majalisar Tarayya
Kotun daukaka kara da ke Abuja ta soke zaben Emmanuel Ukpong-Udo a matsayin dan majalisar wakilai a jihar Akwa Ibom
Kotun daukaka karar ta ce matakin da INEC ta dauka na bayyana dan Majalisar a matsayin wanda ya lashe zaben ya saba wa dokar zaben 2022
An fara zaben dan majalisar wakilan a shekarar 2019 a karkashin jam’iyyar PDP, amma daga baya ya koma YPP
Kotun daukaka kara da ke Abuja ta soke zaben Emmanuel Ukpong-Udo a matsayin dan majalisar wakilai mai wakiltar mazabar Ikono/Ini ta jihar Akwa Ibom.
Kotun daukaka kara ta ce matakin da INEC ta bayyana Mista Ukpong-Udo a matsayin wanda ya lashe zaben ya saba wa dokar zabe ta shekarar 2022, dokoki da ka’idoji na gudanar da zaben 2022 da kuma littafin jagorar zaben 2023.