- Jam’iyyar PDP a jihar Sokoto ta karbi hukuncin kotun koli a kan karar da ta shigar gabanta kan zaben gwamnan jihar
- Bisa ga nufin Allah ne kawai ake samun mulki da kuma ci gaba da kasancewa a wasu lokutan da aka kayyade
- A yau ne kotun kolin ta tabbatar da zaben Ahmed Aliyu a matsayin gwamnan jihar Sokoto
Jam’iyyar PDP a jihar Sokoto ta karbi hukuncin kotun koli a kan karar da ta shigar gabanta kan zaben gwamnan jihar a 2023 tare da mutunta sakamakon zaben.
Hakan na kunshe ne a cikin wata sanarwa da jam’iyyar ta fitar a ranar Alhamis mai dauke da sa hannun sakataren yada labaran ta Hassan Sahabi Sanyinnawal.
KARANTA WANNAN: Da Dumi-Dumi: Kotu Ta Tsare Mutane Biyar Masu Biyayya Ga Gwamnan Ribas Fubara
PDP ta bayyana wa wakilinmu a matsayinta na jam’iyyar siyasa mai bin doka da oda, cewar “PDP ta amince da bangaren shari’a a matsayin mai daidaita tsarin mulki kan batutuwan da suka shafi zabe a kasarmu.
“Jam’iyyar mu kuma ta yi imanin cewa bisa ga nufin Allah ne kawai ake samun mulki da kuma ci gaba da kasancewa a wasu lokutan da aka kayyade.
“Saboda haka, muna kira ga mambobin jam’iyyar PDP na jihar Sokoto da su kwantar da hankulansu na gargajiya domin mutunta doka.”
Jam’iyyar ta kuma bukaci mambobinta da su ci gaba da jajircewa wajen ganin jam’iyyar PDP ta samu ci gaba, “kamar yadda jam’iyyarmu ta sadaukar da kanta wajen taka rawar da ta taka wajen tafiyar da mulkin dimokuradiyyar jiharmu mai albarka.
A dangane da haka, jam’iyyar mu za ta sauke nauyin da ya rataya a wuyanta ga jama’a na tabbatar da cewa gwamnatin da ke mulki ta tabbatar da hakkinsu na gudanar da ayyukansu cikin gaskiya da adalci.
“Muna so mu nuna godiyar jam’iyyar ga mambobinmu da daukacin al’ummar jihar Sokoto saboda goyon bayan da suka bayar a lokacin zaben da kuma tsarin shari’a.”
Sai dai jam’iyyar ta yi kira ga masu ruwa da tsaki a fadin jihar nan da su jajirce wajen ganin an bi tsarin dimokuradiyya a cikin harkokin gudanar da mulki a jiharmu.
Haka kuma tana addu’ar Allah ya kara wa jihar Sokoto da Najeriya karfi, inda za a samu zaman lafiya da ci gaba.
A safiyar yau ne kotun kolin ta tabbatar da zaben Ahmed Aliyu a matsayin gwamnan jihar Sokoto.
Da yake karanta hukuncin, mai shari’a Tijani Abubakar ya yi watsi da karar da jam’iyyar PDP da dan takararta na gwamna, Saidu Umar suka shigar, inda ya amince da dalilin kotun kasa.
A farkon watan Oktobar shekarar 2023, kotun sauraron kararrakin zaben gwamnan jihar Sokoto ta tabbatar da zaben Aliyu.
Kwamitin mutum uku na kotun karkashin Mai shari’a Haruna Msheila a hukuncin da ta yanke ya yi watsi da karar Umar na PDP.
Yana kalubalantar nasarar da gwamnan ya samu a zaben gwamna da aka gudanar a ranar 18 ga watan Maris.
A wani labarin kuma, Sai Mun Karbe Mulkin Jihar Akwa Ibom a 2027 — Martanin APC Ga PDP
Jam’iyyar APC reshen Akwa Ibom, ta ce ta tsaya tsayin daka kan ikirarin shugabanta, Sanata Godswill Akpabio
Jam’iyyar ta yi watsi da martanin da jam’iyyar, PDP ta mayar, inda ta zargi shugaban Majalisar dattawa
Ƴan jihar ba za su iya jiran zaben 2027 ya kawo karshen mulkin PDP a Jihar ba, kuma muna ba da tabbacin za mu samar da gwamnan jihar na gaba
Jam’iyyar APC reshen jihar Akwa Ibom, ta ce ta tsaya tsayin daka kan ikirarin shugabanta, Sanata Godswill Akpabio, na kokarin karbar mulkin jihar ta hanyar zabe a 2027.
Jam’iyyar ta yi watsi da martanin da jam’iyyar, PDP ta mayar, inda ta zargi Sanata Akpabio.