Abuja: Musa Ɗan Shekara 16 shiya koya man neman Maza — Cewar Matashi Mai shekaru 36
Wani Ɗan Shekara 36 Dafet Moses yayi zargin cewa Ɗan Shekara 16 Musa Mohammed ya koya masa neman maza bayan an kama shi suna aikata lamarin a Abuja.
Waɗanda ake zargin an kama su ne a ranar Asabar, daga Mazauna unguwar Kubwa , Ƙaramar Hukumar Bwari.
KARANTA WANNAN LABARIN: Yayi Sauri Peter Obi zama Shugaban Ƙasa, kawai dai zai yi Suna ne yanzu — Inji Babangida Aliyu
Da yake jawabi kafin Ƴan Sanda suyi awon Gaba dashi, Moses yace “ban taɓa yin hakan ba, Musa ne yazo waje na, yace yana so na. Bana Son hakan. Shiya koya man. Nace mashi ya barni in samu kwanciyar hankali, amma sai ya riƙa gargaɗi na, dole nayi mashi biyayya.
“Tun daga lokacin, muke ta kwanciya tare. Abinda zance shine Shaidan ne ya kawo hakan, kuma na gargaɗe shi kada ya ƙara zuwa gida na.”
Matashin ya musanta cewa shiya koya wa Moses. A cewar Muhammad, Moses ne yaci zarafin, domin sun sadu sau biyar kafin a kama su, suna aikata lamarin.
Yace “ta yaya zan koya masa. Yana faɗin abinda bashi bane ba. Kowa ne lokaci yake Son ya sadu dani, yana kaini gidan sa dake Kubwa.
“Moses ne ya koya mani, bayan ya gabatar dani ga Abokin sa, Tunde wanda ya riƙa saduwa dani shima.”
Comments 1