Al’ummar Unguwar Mu’azu, Kinkinau, Tudun Wada da Kabala West sun yi kira ga gwamnan jihar Kaduna, Nasir El-rufai da ya fito da hanyoyin samar da ayyukan yi tare da bunkasa walwalar jama’a duk fadin jihar. Mazauna wadannan yankin sun yi wannan kiran ne a yayin ganawarsu da manema labarai, inda suka nuna damuwarsu da yadda rashin aiki a tsakanin matasa a jihar ke kara hauhawa a koyaushe. Suka ce; rashin aikin yi ga matasan da kuma rashin walwalar Malaman tabbas abin damuwa ne. Saifullah Yahaya, da yake taya El-rufai murnar rantsar da shi a wa’adin mulkinsa na biyu, ya shawarci gwamnan da ya duba matsalolin rashin aikin yi da matasa ke fuskanta da kuma rashin walwalar Malamai a jihar. Ya ce; mafi yawan matasan jihar Kaduna, ba su da aikin yi. A don haka yake kira ga gwamnatin jihar da ta bullo da hanyoyin da matasa za su samu ayyukan yi, domin a cewarsa yin hakan zai rage ayyukan bata gari a jihar. Haka zalika shi ma Anche Daniel, ya shawarci gwamnati da ta sanya bukatun al’umma ne a gabanta wajen daukar matakai, inda ya tabbatar da cewa matasa jigo ne da za su taka muhimmiyar rawa wajen magance matsalolin ayyukan bata gari a jihar. Shima Abduljalal Abdullahi na kungiyar ‘Youth Eco System Support and Social-Development Initiative,’ ya shawarci gwamnan da ya ci gaba da ayyukan da ya faro a tsawon shekarun mulkinsa, ind aya yiwa gwamnan addu’ar samun basirar ci gaba da jagorantar al’ummar Kaduna.